DCL Hausa Radio
Kaitsaye

Gwamnonin PDP sun cimma matsaya da Wike don ceto jam’iyyar kafin zaben 2027

-

Rahotanni daga majiyoyi masu tushe sun tabbatar da cewa akwai sabuwar yarjejeniya tsakanin wasu gwamnonin jam’iyyar PDP da Ministan Babban Birnin Tarayya (FCT), Nyesom Wike, da nufin kawo zaman lafiya da hadin kai cikin jam’iyyar kafin babban zaben shugaban kasa na 2027.

Wani babban jigo daga cikin jam’iyyar ya shaida wa Sunday Punch cewa Gwamnan Jihar Oyo, Seyi Makinde, ne ya wakilci gwamnonin PDP a wani muhimmin zama da suka yi da Wike a birnin Legas makon jiya.

Google search engine

Majiyar ta bayyana cewa taron ya maida hankali ne kan rikicin siyasa da ke faruwa a jihar Ribas tsakanin Wike da gwamnan da aka dakatar Siminalayi Fubara. Haka kuma sun tattauna batutuwan shugabancin yankin Kudu maso Kudu na jam’iyyar da kuma mukamin Sakataren jam’iyya na kasa da har yanzu ba a warware ba tun Disambar 2024.

Jam’iyyar PDP dai tana fama da rikice-rikice na cikin gida tun bayan kammala zaben 2023, kuma yunkurin sulhu da kwamitocin jam’iyyar – ciki har da NWC, BOT, NEC da kuma Gwamnonin PDP – suka yi, ya ci tura, maimakon magance matsalolin sai kara rura wutar rikici.

LEAVE A REPLY

Please enter your comment!
Please enter your name here

Sabbin Labarai

Za mu hada kai wajen magance matsalar tsaron da ta addabi Nijeriya – sabbin hafsonshin tsaron Nijeriya

Sabbin hafsoshin tsaron Nijeriya sun ce za su yi aiki tare domin magance dukkan barazanar tsaro a faɗin kasar, tare da kare martabar ƙasar a...

Gwamnatin Tinubu ta fitar da Naira biliyan 2.3 don biyan bashin albashi da karin girma na malaman jami’o’i

Gwamnatin Tarayya ta bayyana cewa ta saki kudin da ya kai Naira biliyan 2.3 domin biyan bashin albashi da karin girma na malamai a jami’o’in...

Mafi Shahara