DCL Hausa Radio
Kaitsaye

Ana zargin wani matashi ya yi ajalin mahaifinsa a Jigawa

-

Rundunar ‘yan sanda ta kama wani matashi dan shekara 20 mai suna Muhammad Salisu da ake zargin ya yi ajalin mahaifinsa Salisu Abubakar inda ya daddatsa shi da adda a karamar hukumar Gwaram ta jihar Jigawa.

Da yake tabbatar da faruwar lamarin a wata sanarwa da aka rabawa manema labarai a Dutse, a ranar Litinin, jami’in hulda da jama’a na rundunar ‘yan sandan jihar, Shi’isu Adam, ya ce lamarin ya faru ne da misalin karfe 10 na safe a unguwar Bakin Kasuwa da ke yankin Sara.

Google search engine

A cewar kakakin, wanda ake zargin ya yi amfani da adda, inda ya yi wa mahaifinsa munanan raunuka a kafada, wuyansa, da kuma kirji.

Nan take aka garzaya da shi babban asibiti da ke Birnin Kudu, sai dai a can ne Likita ya tabbatar da mutuwarsa.

LEAVE A REPLY

Please enter your comment!
Please enter your name here

Sabbin Labarai

Kotun kolin Nijeriya ta yi watsi da karar da ake zargin Manjo Al Mustapha da hannu wajen halaka matar Abiola

Kotun Kolin Nijeriya ta yi watsi da shari’ar da aka shigar da Manjo Hamza Al Mustapha, kan zarginsa da hannu wajen halaka Kudirat Abiola, matar...

Sojojin da suka yi juyin mulki a Guinea Bissau sun saka ƙarshen shekarar 2026 don gudanar da zaɓe a ƙasar

Sojojin da suka yi juyin mulki a Guinea-Bissau sun ce za a gudanar shugaban ƙasa a ranar 6 ga Disambar 2026, bayan da suka kifar...

Mafi Shahara