DCL Hausa Radio
Kaitsaye

Na bar PDP ne don cigaba da dangwalar arzikin da ke cikin kujerar da nake rike da ita – Shugaban majalisar dokokin jihar Edo

-

Shugaban Majalisar Dokokin Jihar Edo, Rt. Hon. Blessing Agbebaku, ya bayyana dalilin da ya sa ya fice daga jam’iyyar PDP zuwa jam’iyyar APC.

Agbebaku, tare da wasu ‘yan majalisa biyu — Hon. Sunday Fada Eigbiremonlen da Hon. Idaiye Yekini Oisayemoje — sun sanar da sauya shekar su zuwa jam’iyyar APC a ranar Talata.

Google search engine

A yayin da yake sanar da wannan mataki a zauren majalisar a ranar Laraba, Agbebaku ya ce sauya shekar tasa ya samo asali ne daga niyyarsa ta ci gaba da rike kujerar shugaban majalisa domin amfanin mazabarsa.

Shugaban majalisar ya jaddada cewa sauya shekar ba don wani amfani na kai ba ne, illa dai kishin ci gaban al’umma da yankin da ya fito.

LEAVE A REPLY

Please enter your comment!
Please enter your name here

Sabbin Labarai

Manyan Jami’an soji za su fuskanci ritayar dole bayan sauye-sauye a fannin tsaron Nijeriya

Rahotanni sun tabbatar da cewa akwai manyan jami'an sojin Nijeriya  masu mukamin Janar akalla 60 da za su fuskanci ritayar dole, biyo bayan sauye-sauyen da...

Rashin gogewar siyasa ta sa ban tsayar da El-Rufa’i don ya gaje ni ba – Obasanjo

Tsohon shugaban Nijeriya Olusegun Obasanjo ya bayyana cewa ya ki tsayar da tsohon gwamnan jihar Kaduna Malam Nasiru Elrufa'i don ya gaje a shekarar 2007...

Mafi Shahara