DCL Hausa Radio
Kaitsaye

An kama tsohon kwamishina a lokacin El-Rufai kwanaki kadan bayan ficewar sa daga jam’iyyar APC

-

Malam Nasir El – Rufa’i

Jami’an tsaro sun kama tsohon kwamishina a gwamnatin tsohon gwamna Nasir El-Rufai a Kaduna Jafaru Ibrahim Sani, ranar Alhamis.

Google search engine

Rahotanni sun bayyana cewa jami’an Operation Fushin KADA ne suka kama shi da misalin karfe 10:45 na safe, jim kadan da barin gidansa da ke cikin babban birnin jihar.

Wasu majiyoyi sun shaida wa Daily Trust cewa bayan kama shi, an kai shi kotu da ke kan titin Daura, Kaduna, kafin a tsare shi a gidan gyaran hali.

Sani dai na daya daga cikin tsofaffin kwamishinoni shida da suka fice daga jam’iyyar APC mai mulki a kwanakin baya, inda suka bi sahun mai gidan su El-Rufai wanda shi ma ya fice daga jam’iyyar.

Daily Trust ta bayyana cewa an tuntubi jami’in hulda da jama’a na rundunar ‘yan sandan jihar Kaduna, DSP Mansir Hassan, amma ba a samu jin ta bakin shi ba

El-Rufai dai ya alakanta kamun Sani da bita da kullun siyasa, ciki har da ficewarsa daga APC da kuma komawarsa jam’iyyar SDP.

LEAVE A REPLY

Please enter your comment!
Please enter your name here

Sabbin Labarai

Jam’iyyar ADC ta fara rajista da tantance mambobi na kwanaki 90 a fadin Nijeriya

Jam’iyyar African Democratic Congress (ADC) ta fara shirin rajista, tantancewa da kuma jawo sabbin mambobi na tsawon kwanaki 90 a fadin Nijeriya, domin karfafa jam’iyyar...

Ya kamata a haramta amfani da kafafen sada zumunta ga ’yan kasa da shekara 16 a Nijeriya – Femi Falana

Babban lauya kuma SAN, Femi Falana, ya bukaci a haramta amfani da kafafen sada zumunta ga yara ’yan kasa da shekara 16 a Nijeriya, yana...

Mafi Shahara