DCL Hausa Radio
Kaitsaye

Gwamnonin PDP sun kira taron kan sauyin sheka da jiga-jigan jam’iyyar ke yi

-

Gwamnonin jam’iyyar PDP za su yi taro a Abuja akan sauyin shekar da ‘yan jam’iyyar ke yi a kwanakinnan.

Wannan ya biyo bayan ficewar gwamnan jihar Delta Sheriff Oborevwori da Dr. Ifeanyi Okowa, da sauran ‘yan jam’iyyar PDP a jihar zuwa jam’iyyar APC mai mulki.

Gwamnonin sun gana makonni uku da suka gabata a Ibadan inda suka bayyana cewa jam’iyyar ba za su shiga tattaunawar hadaka da tsohon dan takarar shugaban kasa na jam’iyyar PDP a zaben 2023, Alhaji Atiku Abubakar ke jagoranta ba.

Gwamnonin za su yi taron ne a gidan gwamnan jihar Bauchi Bala Abdulkadir Muhammad da ke Asokoro a Abuja da nufin shawo kan matsalolin da suka dabaibaye jam’iyyar.

LEAVE A REPLY

Please enter your comment!
Please enter your name here

Sabbin Labarai

Kada mahajjaci ya rike kudin da suka wuce Riyal 60,000 a kasar Saudiyya – Jan hankalin NAHCON ga Alhazan Nijeriya

Hukumar kula da aikin hajji ta Nijeriya NAHCON ta shawarci mahajjatan kasar da su guji daukar kudi sama da Riyal 60,000 na Saudiyya domin...

Mun yi kuskure a sakamakon da muka fitar na dalibai – Hukumar JAMB

Cikin alhini da nadamar abin da ya faru, hukumar JAMB da ke shirya jarabawar neman shiga makarantun gaba da sakandare a Nijeriya ta karbi duk...

Mafi Shahara