DCL Hausa Radio
Kaitsaye

Lauyoyi sun maka sanatoci a kotu don neman a karbo wani kaso na albashinsu saboda gazawa a aiki

-

Wata kungiya mai suna Association of Legislative Drafting and Advocacy Practitioners (ALDRAP) ta shigar da kara a gaban Kotun Kare Hakkin Masu Sayayya, tana neman tilasta wa sanatocin Najeriya mayar da wani kaso mai yawa na albashinsu tun daga 2023, bisa zargin rashin tabuka abin kirki a majalisa.

Kungiyar a cewaar rahoton da jaridar Punch ta fitar tana neman a karbo cikakken albashin sanatoci 40 da suka rike kujeru a Majalisar Dattawa da kuma Majalisun ECOWAS da Afirka, wanda suka yi rufa-rufa a aiyukan mazabunsu.

Google search engine

A cewar sanarwar da sakataren gudanarwa na ALDRAP, Amuga Williams, ya aika wa shugaban majalisar, Godswill Akpabio a ranar 26 ga Mayu, hakkin ‘yan Nijeriya ne su ci gajiyar ayyukan mazabu daga majalissa, kuma sun dauki matakin ne a madadinsu.

LEAVE A REPLY

Please enter your comment!
Please enter your name here

Sabbin Labarai

China ta umurci matatun man fetur din ta su dakatar da jigilar sa saboda rikicin Gabas ta tsakiya

Gwamnatin China ta umurci manyan matatun man fetur na ƙasar da su dakatar da fitar da dizal da fetur zuwa ƙasashen waje na ɗan lokaci,...

Jami’ar gwamnatin tarayya da ke Dutse a jihar Jigawa ta kori dalibai 20 tare da dakatar da wasu 15 bisa zarginsu da satar jarrabawa

Jami'ar tarayya da ke jihar Jigawa ta kori dalibai 20 tare da dakatar da wasu 15 daga karatu bisa samunsu da laifin satar jarabawa. Rahotanni sun...

Mafi Shahara