DCL Hausa Radio
Kaitsaye

Nacin ciyo bashi da gwamnatin Tinubu ke yi hadari ne ga goben Nijeriya – Atiku Abubakar

-

Tsohon Mataimakin Shugaban Kasa, Atiku Abubakar, ya zargi gwamnatin Tinubu da yawan karbar bashi, yana mai cewa hakan barazana ce ga makomar kasar.

A wani sako da ya wallafa a shafinsa na X, Atiku ya bayyana sabuwar bukatar bashin dala biliyan 21.5, da Yuro biliyan 2.19, da Yeng biliyan 15 da kuma tallafin Yuro miliyan 65 a matsayin “cin amanar tattalin arziki.”

Google search engine

Ya ce bashin Najeriya na iya kaiwa Naira tiriliyan 183 daga Naira tiriliyan 144.7 da aka ruwaito a karshen 2024, yana mai zargin gwamnati da amfani da bashi wajen biyan bashi maimakon ci gaban kasa.

Atiku ya bukaci majalisa, kungiyoyin farar hula, kafofin watsa labarai da kasa da kasa su dakatar da shirin.

LEAVE A REPLY

Please enter your comment!
Please enter your name here

Sabbin Labarai

Babu adawa a jihar Plateau a zaben 2027 – Caleb Muftwang

Gwamnan Jihar Plateau, Caleb Manasseh Mutfwang, ya bayyana cewa zuwa zaben 2027 jam’iyyarsa ba za ta samu adawa a jihar ba. Ya fadi hakan ne...

Obasanjo ya musanta rubuta sanarwar mutuwarsa

Tsohon Shugaban Nijeriya, Olusegun Obasanjo, ya musanta wani rubutu da ke yawo a kafafen sada zumunta da ke ikirarin cewa ya fitar da sanarwar mutuwarsa. Rubutun...

Mafi Shahara