DCL Hausa Radio
Kaitsaye

Hukumar zabe ta kasa INEC ta sanya ranar gudanar da zabukan gwamna a jihohin Ekiti da Osun 

-

Shugaban hukumar, Farfesa Mahmood Yakubu, ne ya bayyana hakan a ranar Juma’a, yayin rantsar da sabbin kwamishinonin zabe guda shida da majalisar dokoki ta kasa ta amince da su kwanan nan.

A cewarsa, za a gudanar da zaben gwamna a jihar Ekiti a ranar Asabar, 20 ga Yuni, 2026. Za a fara zaben fidda gwanin ‘yan takara na jam’iyyun siyasa daga ranar 20 ga Oktoba, 2025, sannan a kammala ranar 10 ga Nuwamba, 2025.

Google search engine

Hakanan, jam’iyyu za su rufe shigar da fom din ‘yan takara da yammacin ranar 22 ga Disamba, 2025.

A jihar Osun kuwa, za a gudanar da zaben gwamna a ranar Asabar, 8 ga Agusta, 2026.

LEAVE A REPLY

Please enter your comment!
Please enter your name here

Sabbin Labarai

Babu adawa a jihar Plateau a zaben 2027 – Caleb Muftwang

Gwamnan Jihar Plateau, Caleb Manasseh Mutfwang, ya bayyana cewa zuwa zaben 2027 jam’iyyarsa ba za ta samu adawa a jihar ba. Ya fadi hakan ne...

Obasanjo ya musanta rubuta sanarwar mutuwarsa

Tsohon Shugaban Nijeriya, Olusegun Obasanjo, ya musanta wani rubutu da ke yawo a kafafen sada zumunta da ke ikirarin cewa ya fitar da sanarwar mutuwarsa. Rubutun...

Mafi Shahara