DCL Hausa Radio
Kaitsaye

Hon. Nasir Aminu Bala Ja’oji ya dauki nauyin ‘yan karamar hukumar Tarauni 20 zuwa kasashen waje domin karo karatu

-

 

Hon. Nasir ja’oji

 A wani yunkuri na bunkasa ilimi a karamar hukumar Taruni,Hwanarabil Nasir Aminu Bala Ja’oji ya bayar da tallafin karatu zuwa kasashen waje ga ‘yan asalin karamar hukumar Tarauni guda 20 da suka cancanta a jihar Kano.

Google search engine

Shirin wanda kungiyar Ja’oji Organisation ke jagoranta, zai baiwa wadanda suka ci gajiyar tallafin damar samun digiri na biyu a kasashen ketare, tare da basu ilimi da kwarewa da gogewa.

Da yake jawabi a wajen Hon. Ja’oji, wanda memba ne a majalisar gudanarwa ta Kwalejin Ilimi ta Tarayya da ke Potiskum, ya jaddada muhimmancin ilimi wajen ci gaban kasa, inda ya bayyana cewa tallafawa matasa zai taimaka wajen gina rayuwar su tare da samun kwararrun ma’aikata a Nijeriya.

Ya bayyana cewa shirin bayar da tallafin karatun na da nufin samarda damammaki ga matasan Nijeriya,don suyi fice a duniya, da inganta rayuwarsu.

LEAVE A REPLY

Please enter your comment!
Please enter your name here

Sabbin Labarai

Shugaba Tinubu babbar kyauta ne daga Allah domin gyaran Nijeriya – Yahaya Bello

Tsohon gwamnan jihar Kogi Yahaya Bello ya bayyana shugaban Nijeriya Bola Tinubu a matsayin babbar kyauta da Allah ya ba Nijeriya domin gyaran kasar. Yahaya Bello...

Gwamnatin Nijeriya ta ce cin jarabawar lissafi “Mathematics” wajibi ne ga daliban Sakandare kafin kammalawa

Gwamnatin Nijeriya ta bayyana cewa lallai dukkan ɗalibai masu rubuta jarabawar kammala sakandare su cigaba da rubuta lissafi tare da harshen Turanci a matsayin wajibi. Mai...

Mafi Shahara