DCL Hausa Radio
Kaitsaye

Majalisa ta gindaya sharuddan da Sanata Natasha za ta cika kafin a mayar da ita kan aiki bayan hukuncin kotu

-

Majalisar Dattawan Nijeriya ta gindaya wasu sharudda kafin ta dawo da Sanata Natasha Akpoti-Uduaghan kan kujerarta, bayan wata kotun tarayya da ke Abuja ta soke dakatarwar watanni shida da majalisar ta yi mata.

A hukuncin da ta yanke a ranar Juma’a, Mai shari’a Binta Nyako ta umurci Majalisar Dattawan da ta dawo da Sanata mai wakiltar Kogi ta Tsakiya, inda ta bayyana dakatarwar a matsayin mai tsanani da ya wuce kima.

Google search engine

Da yake mayar da martani kan hukuncin, mai magana da yawun Majalisar Dattawa, Sanata Yemi Adaramodu, ya ce ba za a dawo da Sanata Natasha kai tsaye ba.

Adaramodu ya bayyana cewa hukuncin kotu bai soke ikon tsarin kundin tsarin mulkin da ke ba Majalisar Dattawa damar ladabtar da mambobinta ba.

Ya kara da cewa Majalisar za ta sake zama domin tattauna batun ne kawai bayan Akpoti-Uduaghan ta cika umarnin kotu.

LEAVE A REPLY

Please enter your comment!
Please enter your name here

Sabbin Labarai

Obasanjo ya nuna jarumtaka da sadaukarwa wajen yi wa Nijeriya hidima – Shugaba Tinubu

Shugaban Nijeriya Bola Ahmed Tinubu, ya taya tsohon shugaban ƙasar Olusegun Obasanjo murnar cika shekaru 89 da haihuwa. A cikin wata sanarwa da mai magana da...

China ta umurci matatun man fetur din ta su dakatar da jigilar sa saboda rikicin Gabas ta tsakiya

Gwamnatin China ta umurci manyan matatun man fetur na ƙasar da su dakatar da fitar da dizal da fetur zuwa ƙasashen waje na ɗan lokaci,...

Mafi Shahara