DCL Hausa Radio
Kaitsaye

Shugaba Tinubu a tsaye yake kodayaushe don yakar matsalar tsaron da ya gada – Malam Nuhu Ribadu

-

Mai ba shugaban Nijeriya shawara kan harkokin tsaro, Malam Nuhu Ribadu, ya ce gwamnatin Shugaba Bola Tinubu ta dage wajen shawo kan matsalolin tsaro masu tsanani da ta gada.

Nuhu Ribadu ya bayyana hakan ne a wajen bikin cika shekaru 50 da kammala karatu na dalibai karo na 18 a kwalejin horar da hafsan sojoji ta Nijeriya (Nigerian Defence Academy, NDA) da aka gudanar a Abuja.

Google search engine

Ya ce a shekarar 2022, Nijeriya ta kasance a mummunan mataki na hadari, tana fama da dumbin kalubale da suka yi barazana ga hadin kan kasa, zaman lafiya da makoma.

Ya bayyana cewa kalubalen sun hada da matsalar ta’addanci a yankin Arewa maso Gabas, kashe-kashe da hare-hare a Arewa maso Yamma, rikice-rikice a yankin Neja Delta da kuma tashe-tashen hankula na ‘yan awaren kafa kasa a Kudu maso Gabas.

A cewarsa, gwamnatin Tinubu ta dauki matakai masu karfi wajen dawo da tsaro da kuma gina sabon kwarin gwiwar kasa.

LEAVE A REPLY

Please enter your comment!
Please enter your name here

Sabbin Labarai

Obasanjo ya nuna jarumtaka da sadaukarwa wajen yi wa Nijeriya hidima – Shugaba Tinubu

Shugaban Nijeriya Bola Ahmed Tinubu, ya taya tsohon shugaban ƙasar Olusegun Obasanjo murnar cika shekaru 89 da haihuwa. A cikin wata sanarwa da mai magana da...

China ta umurci matatun man fetur din ta su dakatar da jigilar sa saboda rikicin Gabas ta tsakiya

Gwamnatin China ta umurci manyan matatun man fetur na ƙasar da su dakatar da fitar da dizal da fetur zuwa ƙasashen waje na ɗan lokaci,...

Mafi Shahara