DCL Hausa Radio
Kaitsaye

Shugaba Tinubu a tsaye yake kodayaushe don yakar matsalar tsaron da ya gada – Malam Nuhu Ribadu

-

Mai ba shugaban Nijeriya shawara kan harkokin tsaro, Malam Nuhu Ribadu, ya ce gwamnatin Shugaba Bola Tinubu ta dage wajen shawo kan matsalolin tsaro masu tsanani da ta gada.

Nuhu Ribadu ya bayyana hakan ne a wajen bikin cika shekaru 50 da kammala karatu na dalibai karo na 18 a kwalejin horar da hafsan sojoji ta Nijeriya (Nigerian Defence Academy, NDA) da aka gudanar a Abuja.

Google search engine

Ya ce a shekarar 2022, Nijeriya ta kasance a mummunan mataki na hadari, tana fama da dumbin kalubale da suka yi barazana ga hadin kan kasa, zaman lafiya da makoma.

Ya bayyana cewa kalubalen sun hada da matsalar ta’addanci a yankin Arewa maso Gabas, kashe-kashe da hare-hare a Arewa maso Yamma, rikice-rikice a yankin Neja Delta da kuma tashe-tashen hankula na ‘yan awaren kafa kasa a Kudu maso Gabas.

A cewarsa, gwamnatin Tinubu ta dauki matakai masu karfi wajen dawo da tsaro da kuma gina sabon kwarin gwiwar kasa.

LEAVE A REPLY

Please enter your comment!
Please enter your name here

Sabbin Labarai

Kamfanin NNPCL ya musanta labarin cefanar da matatar man birnin Port Harcourt

Kamfanin man fetur na Nijeriya NNPCL ya musanta labarin cefanar da matatar mai ta Fatakwal ga yan kasuwa A Yayin wani taro da kamfanin ya gabatar...

Tattalin arzikin Najeriya zai bunkasa daga 2025 zuwa 2026 – IMF

Asusun Lamuni na Duniya (IMF) ya sabunta hasashensa kan ci gaban tattalin arzikin Najeriya, inda ya ce zai kai kashi 3.4 cikin 100 a shekarar...

Mafi Shahara