DCL Hausa Radio
Kaitsaye

Ba da gan-gan harin da muke kai wa ‘yan ta’adda ke shafuwar fararen hula ba – Sojojin Nijeriya

-

 Ba da gan-gan harin da muke kai wa ‘yan ta’adda ke shafuwar fararen hula ba – Sojojin Nijeriya

Google search engine

Rundunar sojin Najeriya ta ce duk hare-hare ta sama da take kai wa ga masu aikata laifukan ne ba fararen hula ba.

Babban Hafsan Sojojin Najeriya Janar Christopher Musa ne ya bayyana haka a wata hira da yayi a gidan Talabiji na Arise TV, a lokacin da yake mayar da martani game da mutuwar fararen hula sama da 10 sanadiyar harin da sojojin suka kai kwanan nan a Zamfara.

Janar Christopher Musa, wanda ya bayyana cewa sojoji sun bi ka’idoji masu tsauri kafin aiwatar da duk wani hari ta sama, ya jaddada cewa sojojin na kai hare-hare ta sama daidai gwargwado domin kawar da yan ta’adda dake addabar wasu sassan jihohin Nijeriya.

LEAVE A REPLY

Please enter your comment!
Please enter your name here

Sabbin Labarai

Jam’iyyar ADC ta fara rajista da tantance mambobi na kwanaki 90 a fadin Nijeriya

Jam’iyyar African Democratic Congress (ADC) ta fara shirin rajista, tantancewa da kuma jawo sabbin mambobi na tsawon kwanaki 90 a fadin Nijeriya, domin karfafa jam’iyyar...

Ya kamata a haramta amfani da kafafen sada zumunta ga ’yan kasa da shekara 16 a Nijeriya – Femi Falana

Babban lauya kuma SAN, Femi Falana, ya bukaci a haramta amfani da kafafen sada zumunta ga yara ’yan kasa da shekara 16 a Nijeriya, yana...

Mafi Shahara