DCL Hausa Radio
Kaitsaye

Ministan Abuja Wike ya kwace filayen tsohon shugaban kasa Buhari, Tajudeen Abbas, George Akume da wasu manyan mutane 759

-

Ministan babban birnin tarayya Abuja Nyesom Wike, ya kwace filaye tsohon shugaban kasa Muhammad Buhari, da kakakin majalisar dokoki Tajudeen Abbas da kuma Sakataren gwamnatin tarayya George Akume.
Hakama Wike ya kwace filayen wasu manyan mutane da kungiyoyi 759 a yankin Maitama II, Abuja saboda saboda kin biyan kudaden takardar mallaka.
Wannan na kunshe ne a cikin wata sanarwa har biyu da hukumar kula da babban birnin tarayya Abuja ta aikewa gidan talabijin na Channels.
Daya sanarwar ta ce, ministan ya yi barazanar kwace filayen jagoran marasa rinjaye na majalisar wakilai Kingsley Chinda da tsofaffin shugabannin majalisar dattawa Iyorchia Ayu da Ameh Ebute da mai tsawatarwa na majalisar dattawa Tahir Monguno; kazalika da wasu sanannun mutane 610, idan har ba su biyu kudaden ba cikin makonni biyu.

LEAVE A REPLY

Please enter your comment!
Please enter your name here

Sabbin Labarai

’Yan majalisar wakilai bakwai daga Akwa Ibom sun sauya sheka zuwa APC

Ana cigaba da samun rahotannin sauyin sheka a majalisar wakilai, yayin da ’yan majalisa bakwai daga Jihar Akwa Ibom suka koma jam’iyyar APC. Wadanda suka...

Jam’iyyar Labour tsagin Julius Abure ta ba Peter Obi sa’o’i 48 ya fice daga jam’iyyar saboda shiga hadakar ADC

Jam’iyyar Labour karkashin jagorancin Julius Abure ta bai wa tsohon dan takarar shugaban kasa, Peter Obi, wa’adin sa’o’i 48 da ya fice daga jam’iyyar, bisa...

Mafi Shahara