DCL Hausa Radio
Kaitsaye

Rundunar ‘yan sandan jihar Kano ta kama mutane biyu da ake zargi da satar Keke-napep

-

Rundunar ‘yan sandan jihar Kano ta kama wasu mutum biyu da ake zargi da satar Keke-napep tare da hannunta ababen hawan da ta gano ga masu su.
A cewar wani bayani da kakakin rundunar SP Abdullahi Haruna ya fitar, rundunar ta samu wannan nasara ne bayan wani samame da ta kai a maboyar bata garin da ke karamar hukumar Dambatta a ranar 9 ga watan Disamban da muke ciki.
A yayin samamen an kama wani Ado Yusuf, mai shekaru 40 da kuma Rabi’u Suleiman, mai shekaru 35, tare da kwato Keke-napep biyu da aka sace.

LEAVE A REPLY

Please enter your comment!
Please enter your name here

Sabbin Labarai

Majalisar dattawa ta bukaci a dauki matasa aikin tsaro domin magance matsalar tsaro

Majalisar dattawan Nijeriya, ta nuna damuwa kan tabarbarewar tsaro a ƙasar, tana kira ga shugaban ƙasa Bola Tinubu da ya amince da daukar matasa akalla...

Matukar dimokradiyya ta gaza a Nijeriya sai ya shafi fadin Yammacin Afrika – ECOWAS

Kungiyar tattalin arzikin kasashen Yammacin Afrika, ECOWAS, ta gargadi cewa duk wani rauni da dimokuradiyya ta samu a Nijeriya zai yi sanadin rushewar tsarin a...

Mafi Shahara