Tuesday, April 7, 2026
HomeLabarai‘Yan bindiga sun yi garkuwa da makusancin Yahaya Bello na Kogi

‘Yan bindiga sun yi garkuwa da makusancin Yahaya Bello na Kogi

Kabiru Onyene makusancin tsohon gwamnan Kogi 

Rahotanni daga jihar Kogi na nuni da cewa, an sace Kabir Onyene, ne da misalin karfe 7 da mintuna 5 na yammacin ranar Litinin, lokacin da wasu ‘yan bindiga dauke da bindigogi suka farmaki ofishinsa da ke Okene a jihar, inda suka yi ta harbe-harbe kafin daga bisani su yi awon-gaba da shi. 

Bayanai sun nuna cewa yayin harin, an harbe wani mutum wanda kawo yanzu ba a tantance ko wanene ba.

Sai dai har kawo yanzu rundunar ‘yan sandan jihar ta Kogi ba ta ce uffan, kan lamarin ba.

RELATED ARTICLES

LEAVE A REPLY

Please enter your comment!
Please enter your name here

Most Popular

Recent Comments

Mustapha madu bande on Tarihin marigayi Aminu Dantata