DCL Hausa Radio
f DCL HAUSA FACEBOOK
Tuesday, April 21, 2026
Home Blog Page 125

Nijeriya a shirye take ta karbi taimakon Amurka wajen yaki da ‘yan bindiga muddin za a mutunta ‘yancinta – Gwamnatin Nijeriya

0

Biyo bayan barazanar da shugaban Amurka, Donald Trump ya yi na ɗaukar matakin soja kan zargin cin zarafin Kiristoci a Nijeriya, gwamnatin Nijeriya ta ce za ta yi maraba da taimakon Amurka wajen yaƙi da ‘yan ta’adda muddin za a mutunta cikakken ‘yancinta na cikin gida.

Trump ya wallafa a shafinsa cewa ya umurci ma’aikatar tsaron Amurka ta shirya matakin gaggawa idan Nijeriya ta gaza dakatar da kisan Kiristoci, tare da barazanar dakatar da duk wani tallafi kamar yadda Aljazeera ta ruwaito.

Mai magana da yawun fadar shugaban kasa, Daniel Bwala, ya ce Nijeriya za ta karɓi duk taimako muddin ana mutunta huruminta, yana mai cewa taron da ake shirin gudanarwa tsakanin Tinubu da Trump zai taimaka wajen ƙarfafa haɗin kai kan yaƙi da ta’addanci.

Tun da farko dai, shugaba Bola Tinubu ya musanta zargin wariyar addini, yana mai cewa gwamnatinsa tana aiki tare da shugabannin addinai don tabbatar da tsaro da kare ‘yancin kowane ɗan ƙasa, Musulmi ko Kirista.

Shugaba Tinubu na amfani da karfi ga ‘yan adawa domin sauya sheka zuwa APC, in ji jam’iyyun adawa a Nijeriya

0

Wasu jam’iyyun adawa a Nijeriya na zargin Shugaba Bola Tinubu da amfani da kudaden gwamnati da hukumomin yaƙi da cin hanci da rashawa domin tilasta wa ‘yan adawa su koma jam’iyyar APC.

A cewar kakakin jam’iyyun PDP, NNPP da CUPP, wato Debo Ologunagba, Oladipo Johnson, da Mark Adebayo, sauya shekar da ake ta gani daga ‘yan adawa zuwa APC na nuna cewa jam’iyyar mai mulki na dab da rugujewa daga ciki.

Sai dai kakakin yaɗa labarai na APC, Bala Ibrahim, ya karyata zargin, yana mai cewa wadanda suka koma jam’iyyar sun yi hakan ne da son ransu saboda irin nasarorin da APC ke samu a mulki, kuma jam’iyyar na da cikakken tsari da zai hana ta fadawa rikicin cikin gida.

Zargin Trump na kisan Kiristoci a Nijeriya ba gaskiya ba ne, cewar wani lauya a Nijeriya

0

Wani lauya kuma tsohon mai ba da shawara ga shugaban kasa, Chief Okoi Obono-Obla, ya zargi Shugaban Amurka Donald Trump da wasu bangarorin gwamnatin Amurka da yin nuni da karya da kuma raini kan zargin cewa ana kisan Kiristoci a Nijeriya.

Yayin da yake magana a Calabar a ranar Lahadi, Obono-Obla ya bayyana matakin Amurka a matsayin diplomasiyya mai cike da ruɗani wadda ke nuna girman kai da son nuna karfi, yana mai cewa Amurka na amfani da batun addini ne domin kawo rudani a Nijeriya.

Okoi ya kara da cewa, ita kanta Amurka na fama da hare-haren ‘yan bindiga a majami’u amma ba ta bukaci sojojin kasashen waje su shigo mata ba, to bai kamata ta tsoma baki cikin harkokin cikin gida na Nijeriya ba.

Jaridar Daily Trust ta ruwaito cewa, lauyan ya gargadi Amurka da cewa duk wani yunƙuri na kutse a cikin harkokin Nijeriya da sunan kare addini zai zama karya doka a matakin kasa da kasa.

Nijeriya za ta karbi bashin Dala biliyan daya daga bankin duniya

0

Bankin Duniya ya shirya amincewa da bashin dala biliyan ɗaya ga Nijeriya a ranar 16 ga watan Disamba, ƙarƙashin shirin saka hannun jari da samar da ayyukan yi a Nijeriya.

Bashin, wanda ya ƙunshi dala miliyan 500 na IDA da dala miliyan 500 na IBRD, zai tallafa wa sauye-sauyen tattalin arziki, samar da ayyukan yi, da ƙarfafa saka hannun jari daga kamfanoni masu zaman kansu.

A cewar bankin, za a gudanar da shirin ta ma’aikatar Kudin Nijeriya, don taimaka wa Nijeriya ta tashi daga matakin farfaɗo da tattalin arziki zuwa ci-gaba mai ɗorewa ta hanyar rage hauhawar farashi da bunƙasa fitar da kayayyaki zuwa kasashen ketare kamar yadda jaridar Punch ta ruwaito.

Jam’iyyar SDP ta jaddada dakatarwar da ta yi ma El-Rufai na tsawon shekaru 30

0

Kungiyar shugabannin jam’iyyar SDP na jihohi 37 ta tabbatar da cewa tsohon Gwamnan Jihar Kaduna, Malam Nasir El-Rufai, har yanzu yana cikin dakatarwa daga jam’iyyar na tsawon shekaru 30.

Wannan sanarwa ta fito ne bayan jita-jitar da ke yawo cewa El-Rufai na shirin komawa cikin jam’iyyar kafin babban taronta na kasa.

Shugaban kungiyar, Femi Olaniyi, ya shaida wa jaridar PUNCH a ranar Lahadi an Abuja cewa, babu komawa baya a kan hukuncin da kwamitin gudanarwa na kasa ya dauka kan El-Rufai.

A cewarsa, El-Rufai ya shiga jam’iyyar ne ta bayan gida kuma tun a ranar 3 ga watan Afrilu, 2025 an bayyana cewa duk wanda ke son shiga jam’iyyar sai ya bi matakin ofishin mazaba da na jiha, amma El-Rufai bai bi wannan hanya ba. Don haka ne kwamitin kasa ya dakatar da shi har na shekaru 30, kuma wannan hukunci ba zai canza ba.

Shugaba Tinubu zai gana da Trump ba da jimawa ba, in ji Daniel Bwala

0

Fadar shugaban Nijeriya ta bayyana cewa shugaba Bola Tinubu da shugaban Amurka, Donald Trump za su gana a cikin ‘yan kwanaki masu zuwa domin tattaunawa kan zargin kisan Kiristoci a kasar.

Wannan na zuwa ne bayan kalaman Trump da suka zargi gwamnatin Nijeriya da rashin daukar mataki kan hare-haren da ake kai wa Kiristoci, inda ya kuma yi barazanar kai hari a Nijeriya da kuma dakatar da tallafin Amurka.

Mai ba shugaban kasar shawara Mr Daniel Bwala ya ce shugabannin biyu na da kyakkyawar alaka wajen yaki da ta’addanci, inda ya kara da cewa gwamnatin Trump ce ta amince da sayar wa Nijeriya makamai, kuma gwamnatin Tinubu ta yi amfani da damar wajen samun gagarumar nasara a yaki da ta’addanci.

PDP Bangaren Wike ya dakatar da Damagum yayin da sabon rikicin shugabanci ya sake kunno kai a jam’iyyar

0

Jam’iyyar PDP ta sake fadawa cikin rikici yayin da sabuwar rarrabuwar kai ta kunno kai a cikin shugabancinta, inda wani bangare mai goyon bayan ministan Abuja, Nyesom Wike, ya sanar da dakatar da mukaddashin shugaban jam’iyyar na kasa, Umar Damagum, da wasu mambobin kwamitin gudanarwa guda biyar.

Da yake jawabi ga manema labarai a Abuja a ranar Asabar a madadin bangaren, sakataren jam’iyyar na kasa, Sanata Samuel Anyanwu, ya bayyana mataimakin shugaban jam’iyyar na yankin Arewa ta Tsakiya, Mohammed Abdulrahman, a matsayin sabon mukaddashin shugaban jam’iyyar.

Anyanwu ya ce an dakatar da Damagum bisa rashin iya aiki, almundahana, da kin bin hukuncin kotu, tare da tura shi gaban kwamitin ladabtarwa na jam’iyyar.

Haka kuma ya kara da cewa an dakatar da mai magana da yawun jam’iyyar, Debo Ologunagba, bisa fitar da sanarwa ba tare da izini ba, sai mataimakin shugaban jam’iyyar na yankin kudu, Taofeek Arapaja, da kuma mai kula da harkokin kudi, Daniel Woyenguikoro, bisa zargin almundahana.

Hakazalika, an dakatar da shugaban matasa na kasa, Sulaiman Kadade, da mataimakin sakataren kasa, Setonji Koshoedo, na tsawon kwanaki 30 kamar yadda jaridar Punch ta ruwaito.

Sai dai a baya, kwamitin karkashin jagorancin Damagum shi ma ya dakatar da Sanata Samuel Anyanwu, lauyan jam’iyyar, Kamaldeen Ajibade (SAN), da wasu mambobi biyu, abin da ya kara tsananta rikicin cikin gida da jam’iyyar ke ciki a halin yanzu.

Jam’iyyar PDP ta dakatar da mambobinta hudu na tsawon wata daya

0

Kwamitin Ayyuka na Kasa na jam’iyyar PDP ya dakatar da mai ba da shawara kan harkokin shari’a na kasa, Kamaldeen Ajibade (SAN), sakataren jam’iyya na kasa, Sanata Samuel Anyanwu, mataimakin mai ba da shawara kan shari’a, Okechukwu Osuoha da kuma sakataren shirya taruka na kasa, Umaru Bature, na tsawon wata guda bayan hukuncin kotu da ya dakatar da taron gangamin jam’iyyar da aka shirya.

Jaridar Punch ta ruwaito mai magana da yawun jam’iyyar, Debo Ologunagba, ne ya bayyana haka yayin da yake magana da manema labarai a ranar Asabar, bayan taron gaggawa da kwamitin ya gudanar a ofishin jam’iyyar da ke a Maitama, Abuja.

Ologunagba ya ce kwamitin ya dauki matakin ne bisa tanadin kundin tsarin jam’iyyar, tare da mika wadanda abin ya shafa ga kwamitin ladabtarwa domin daukar matakin da ya dace.

PDP ta ce za ta daukaka kara kan hukuncin dakatar da babban taronta a Ibadan

0

Jam’iyyar PDP ta ce za ta daukaka kara kan hukuncin kotun tarayya da ta dakatar da gudanar da babban taronta da aka shirya yi a Ibadan, jihar Oyo, a ranar 15 da 16 ga watan Nuwamba.

A wata sanarwa da mai magana da yawun jam’iyyar na kasa, Debo Ologunagba, ya fitar a ranar Juma’a, PDP ta bayyana hukuncin a matsayin kutse ga tsarin dimokuradiyya, tana mai jan hankalin mambobinta da su ci gaba da shirin taron ba tare da rudani ba.

Jam’iyyar ta ce ta umarci lauyoyinta su daukaka kara nan take, tare da jaddada cewa hukuncin bai hana ta ci-gaba da shirye-shiryen gudanar da taron da zai zabi sabbin shugabannin jam’iyyar ba, domin ci-gaba da kare dimokuradiyya a Nijeriya.

Matatar man Dangote ta yi alkawarin samar da wadataccen man fetur a lokacin bukukuwan karshen shekara

0

Matatar man Dangote ta tabbatar da cewa za ta samar da isasshen man fetur da dizal a fadin Nijeriya a lokacin bukukuwan karshen shekara domin a cewar kamfanin, yawan man da ake tacewa a kullum yanzu ya haura abin da ake bukata.

Mai kula da harkokin yada labarai da dabarun kasuwanci na rukunin kamfanonin Dangote, Anthony Chiejina, ne ya bayyana haka cikin wata sanarwa da aka samu daga ofishinsa a ranar Asabar, inda ya ce matatar tana fitar da lita miliyan 45 na fetur da lita miliyan 25 na dizal a kullum.

Chiejina, ya ce kamfanin na aiki tare da hukumomi da masu rarraba man domin tabbatar da isar sa cikin sauki a fadin kasar.

A cewarsa, karuwar tace man a cikin gida na taimakawa wajen karfafa Naira ta hanyar rage kudaden da ake fitarwa waje da kuma karfafa kudaden da ke shigowa cikin gida.