DCL Hausa Radio
f DCL HAUSA FACEBOOK
Sunday, April 19, 2026
Home Blog Page 124

Jam’iyyar PDP ta dakatar da mambobinta hudu na tsawon wata daya

0

Kwamitin Ayyuka na Kasa na jam’iyyar PDP ya dakatar da mai ba da shawara kan harkokin shari’a na kasa, Kamaldeen Ajibade (SAN), sakataren jam’iyya na kasa, Sanata Samuel Anyanwu, mataimakin mai ba da shawara kan shari’a, Okechukwu Osuoha da kuma sakataren shirya taruka na kasa, Umaru Bature, na tsawon wata guda bayan hukuncin kotu da ya dakatar da taron gangamin jam’iyyar da aka shirya.

Jaridar Punch ta ruwaito mai magana da yawun jam’iyyar, Debo Ologunagba, ne ya bayyana haka yayin da yake magana da manema labarai a ranar Asabar, bayan taron gaggawa da kwamitin ya gudanar a ofishin jam’iyyar da ke a Maitama, Abuja.

Ologunagba ya ce kwamitin ya dauki matakin ne bisa tanadin kundin tsarin jam’iyyar, tare da mika wadanda abin ya shafa ga kwamitin ladabtarwa domin daukar matakin da ya dace.

PDP ta ce za ta daukaka kara kan hukuncin dakatar da babban taronta a Ibadan

0

Jam’iyyar PDP ta ce za ta daukaka kara kan hukuncin kotun tarayya da ta dakatar da gudanar da babban taronta da aka shirya yi a Ibadan, jihar Oyo, a ranar 15 da 16 ga watan Nuwamba.

A wata sanarwa da mai magana da yawun jam’iyyar na kasa, Debo Ologunagba, ya fitar a ranar Juma’a, PDP ta bayyana hukuncin a matsayin kutse ga tsarin dimokuradiyya, tana mai jan hankalin mambobinta da su ci gaba da shirin taron ba tare da rudani ba.

Jam’iyyar ta ce ta umarci lauyoyinta su daukaka kara nan take, tare da jaddada cewa hukuncin bai hana ta ci-gaba da shirye-shiryen gudanar da taron da zai zabi sabbin shugabannin jam’iyyar ba, domin ci-gaba da kare dimokuradiyya a Nijeriya.

Matatar man Dangote ta yi alkawarin samar da wadataccen man fetur a lokacin bukukuwan karshen shekara

0

Matatar man Dangote ta tabbatar da cewa za ta samar da isasshen man fetur da dizal a fadin Nijeriya a lokacin bukukuwan karshen shekara domin a cewar kamfanin, yawan man da ake tacewa a kullum yanzu ya haura abin da ake bukata.

Mai kula da harkokin yada labarai da dabarun kasuwanci na rukunin kamfanonin Dangote, Anthony Chiejina, ne ya bayyana haka cikin wata sanarwa da aka samu daga ofishinsa a ranar Asabar, inda ya ce matatar tana fitar da lita miliyan 45 na fetur da lita miliyan 25 na dizal a kullum.

Chiejina, ya ce kamfanin na aiki tare da hukumomi da masu rarraba man domin tabbatar da isar sa cikin sauki a fadin kasar.

A cewarsa, karuwar tace man a cikin gida na taimakawa wajen karfafa Naira ta hanyar rage kudaden da ake fitarwa waje da kuma karfafa kudaden da ke shigowa cikin gida.

Nijar da Chadi na son karfafa dangantakarsu

0

Kasashen Nijar da Chadi sun kammala wani taron hadin gwiwa na kwanaki biyu da suka gudanar a birnin N’djamena na kasar Chadi karkashin jagorancin Firaministocin kasashen biyu.

A yayin taron kasashen biyu sun kara jaddada dadaddariyar yarjejeniyar dangantakar da ke a tsakaninsu tare da rattaba hannu kan wadansu sabbi.

Nijar da Chadi na da dadaddiyar dangantaka mai kyau a tarihi a matsayin su na kasashe makwabtanta juna.

Matsalar Nijeriya ba ta addini ba ce illa rashin shugabanci nagari – Sowore

0

Dan gwagwarmayar kare hakkin dan’Adam kuma tsohon dan takarar shugaban kasa, Omoyele Sowore, ya mayar da martani ga kalaman shugaban Amurka, Donald Trump da ya bayyana cewa Kiristoci na fuskantar barazana a Nijeriya.

A wani sakon da ya wallafa a shafinsa na X a ranar Asabar, Sowore ya ce ceto Nijeriya ba zai fito daga waje ba, sai dai daga ingantaccen shugabanci a cikin gida. Sannan matsalar Nijeriya ba ta takaita ga addini ba, illa sakacin gwamnati, cin hanci, da rashin shugabanci mai nagarta.

Jaridar Punch ta ruwaito Sowore ya kara da cewa duka Kiristoci da Musulmai na fama da hare-haren ‘yan bindiga da talauci a sassa daban-daban na kasar, maimakon a rika kallon matsalolin tsaro ta fuskar addini, lokaci ya yi da ‘yan Nijeriya za su hada kai wajen neman shugabanci nagari da kare rayukan jama’a.

Nijeriya ta musanta zargin Trump kan kisan Kiristoci a kasar

0

Gwamnatin Nijeriya ta musanta maganganun shugaban Amurka, Donald Trump, da ke cewa ana yawan kisan Kiristoci a Nijeriya tare da kiranta “kasa mai matsalar tauye ‘yancin addini.”

A cikin wata sanarwa da mai magana da yawun ma’aikatar harkokin wajen Nijeriya, Kimiebi Ebienfa, ya fitar a safiyar Asabar, gwamnatin ta ce wadannan zarge-zargen ba su da tushe kuma ba su bayyana ainihin halin da ake ciki a kasa ba.

Sanarwar ta kara da cewa, karkashin shugabancin Bola Ahmed Tinubu, Nijeriya na ci gaba da yaki da ta’addanci tare da karfafa zaman lafiya da fahimtar juna tsakanin addinai, da kuma kare rayuka da hakkin ‘yan kasa kamar yadda jaridar Punch ta ruwaito.

Hakazalika, sanarwa ta ce gwamnatin Nijeriya za ta cigaba da tattaunawa da gwamnatin Amurka domin kara fahimtar juna kan kokarin da ake yi wajen tabbatar da zaman lafiya da tsaro a yankin.

Yadda fitinar bayan zabe ta yi ajalin mutane sama da 700 a Tanzaniya

Jam’iyyar adawa ta Chadema a Tanzaniya ta bayyana cewa fiye da mutane 700 ne suka mutu cikin kwana uku na zanga-zangar bayan zaɓen shugaban ƙasa, wadda ta haifar da tarzoma da tsaurara matakan tsaro a fadin ƙasar.

A cewar rahoton jaridar Daily Trust, zaɓen ya gudana ne cikin tashin hankali, katsewar intanet da kulle hanyoyin sadarwa, lamarin da ya sa ake diga ayar tambaya kan sahihancin zaɓen da gaskiyar sakamakon.

DCL Hausa ta ruwaito cewa, shugabar Tanzaniya Samia Suluhu Hassan, mai shekara 65, wadda ke neman wa’adin farko cikakke a ƙarƙashin jam’iyyar Chama Cha Mapinduzi (CCM), ta fuskanci hamayya daga ‘yan takara 16. Sai dai hana wasu manyan ‘yan adawa shiga takara da shari’o’in da ke ci gaba, sun jefa shakku cikin tsarin.

Kakakin jam’iyyar Chadema, John Kitoka, ya shaida wa kamfanin dillancin labaran Faransa na AFP cewa adadin mutanen da suka mutu a babban birnin kasar, Dar es Salaam ya kai kusan 350, yayin da a a birnin Mwanza ya wuce 200. AFP ya ce jimillar ta kai kusan 700, kuma “na iya ƙaruwa” saboda an kafa dokar hana fita da dare tun ranar Laraba.

Tinubu ya umurci sabbin hafsoshin tsaro da su murƙushe duk wata barazanar tsaro

0

Shugaban kasa Bola Ahmed Tinubu ya umurci sabbin hafsoshin tsaron da su tashi tsaye wajen murƙushe duk wata barazanar tsaro da ke tasowa a sassan Nijeriya.

Da yake bayani bayan tattabatar dasu a fadarsa a Alhamis dinnan, Tinubu ya ce barazanar tsaro na ta karuwa, kuma abin damuwa shi ne fitowar sabbin kungiyoyin ‘yan ta’adda a yankunan Arewa ta tsakiya, Arewa maso yamma da kuma wasu sassa na Kudu.

Ya ƙara da cewa ‘yan Nijeriya na bukatar zaman lafiya cikin gaggawa, don haka ya bukaci hafsoshin su yi aiki da kishin ƙasa.

Sojojin da ake tsare da su bisa zargin juyin mulki a Nijeriya sun kai 42 a wani binciken jaridar Daily Trust

Yawan sojojin da ake tsare da su bisa zargin yunƙurin juyin mulki ya ƙaru zuwa 42, kamar yadda majiyoyi daga cikin rundunar sojin suka tabbatar wa jaridar Daily Trust.

Majiyoyin sun shaida wa jaridar Daily Trust cewa, har yanzu ana ci gaba da gano yadda kowannensu ya taka rawa da yadda shirin ya faro.

Majiyar ta kara da cewa hukumar leken asiri ta sojoji DIA da na ci gaba da bin diddigin lamarin,yayin adadin wadanda ake zargi ya karu daga 16, zuwa 42.

Sai dai mai bai wa shugaba Tinubu shawara kan harkokin yaɗa labarai, Sunday Dare, ya ce fadar shugaban kasa na tare da matsayar rundunar tsaron kan wannan batu.

Barayin daji sun yi ajalin Dagacin kauye a jihar Sokoto

0

‘Yan bindiga sun kai mummunan hari a kauyen Kurawa, karamar hukumar Sabon Birni da ke jihar Sokoto, inda suka halaka mutane uku ciki har da dagacin kauyen.

Jaridar Daily Trust ta rawaito cewa lamarin ya faru ne da misalin ƙarfe 12 na dare, inda maharan suka kai farmaki bayan sun rushe katangar da mutane suka yi a matsayin kariya daga hare-hare.

Wani mazaunin yankin ya shaida cewa sun samu bayani daga wani kauye a makwabta cewa ‘yan bindiga na kan hanyarsu zuwa Kurawa, inda suka hanzarta sanar da hukumomin tsaro.

Duk da haka, bayan da ‘yan bindigar sun shiga kauyen, suka fara harbe-harbe na kusan mintuna 30, inda jami’an tsaro da vigilante suka yi ƙoƙarin fatattakar su.

Sai dai duk da hakan, dagacin garin, Hussaini Alhaji Yawalle, da wasu mutum biyu sun mutu a harin.