Sunday, April 5, 2026
Home Blog Page 2

Muna kira ga ‘yan Nijeriya kar su sake zabar Tinubu saboda gazawa wajen samar da wutar lantarki – Peter Obi 

Tsohon ɗan takarar shugabancin Nijeriya a zaɓen 2023 Peter Obi, ya bukaci ‘yan kasar kada su sake zaɓen Shugaba Tinubu, yana mai danganta hakan da gazawa wajen inganta wutar lantarki a ƙasar.

Obi ya bayyana hakan ne a wani sako da ya wallafa a shafinsa na X, inda ya tuna cewa Tinubu ya yi alkawarin idan bai samar da wutar lantarki mai dorewa cikin shekaru huɗu ba, kada a sake zaɓensa.

Ya ce a halin yanzu alkawarin bai cika ba saboda samun wutar lantarki ya ragu daga sama da megawatt 4,000 a shekarar 2023 zuwa ƙasa da haka yanzu, yayin da kuma farashin lantarki ke karuwa sossai.

NLC ta bukaci ma’aikatan jihohin da ba su aiwatar da mafi karancin albashi su gudanar da zanga-zanga

Kungiyar ƙwadago a Nijeriya NLC, ta umarci ma’aikata a jihohin da ba su aiwatar da sabon mafi ƙarancin albashi ba, su gudanar da bikin May Day na 2026 a kan tituna maimakon wuraren taro na gwamnati.

A cikin wata sanarwa da Sakataren kungiyar Emmanuel Ugboaja ya fitar, ya zargi wasu gwamnatocin jihohi da karya dokar sabon valbashi ta 2024, musamman wajen rashin biyan cikakken albashi, rashin gyara albashin manyan ma’aikata da kuma kin shigar da ma’aikatan kananan hukumomi, malamai da ma’aikatan lafiya cikin tsarin.

Kungiyar ta bayyana cewa irin wannan mataki na jihohi cin zarafi ne ga hakkin ma’aikata, tare da cewa dokar albashi da Shugaba Bola Tinubu ya rattaba wa hannu wacce ta sauya albashi daga naira 30,000 zuwa 70,000 ba ta samu cikakken aiwatarwa ba a wurare da dama.

NLC ta bukaci ma’aikata su taru daga karfe 7 na safe a ranar 1 ga watan Mayu su fito zanga-zanga cikin lumana a manyan biranen jihohi, inda za su kai korafe-korafensu ga gwamnati, tana mai cewa rashin yin hakan zai zama kamar cin amanar gwagwarmayar ma’aikata.

Gwamna Dauda Lawal ya lashe kyautar gwarzon gwamnan shekara a birnin London

LGwamnan jihar Zamfara Dauda Lawal ya lashe kyautar gwarzon gwamnan shekara ta mujallar ‘Triangle Media International’ a birnin London.

Wata sanarwa da mai magana da yawunsa Sulaiman Bala Idris ya fitar, ta bayyana cewa ana bayar da kyautar ne ga jagorori wadanda tasirin shugabancinsu ya bayyana a zahiri.

Ba za a fara tura wa mahajjatan Nijeriya kudin guzuri ta asusun banki a wannan shekarar ba – NAHCON

Babban Bankin Nijeriya CBN ya amince da amfani da tsabar kuɗi ga alhazan Nijeriya a Hajjin 2026 a matsayin kudin guzuri maimakon tsarin kati da ake shirin fara amfani da shi.

Matakin ya biyo bayan roƙon da Hukumar Alhazai ta ƙasa ƙarƙashin jagorancin Ismail Abba Yusuf ta yi domin rage damuwar maniyyata kan sauyin tsarin.

CBN ta ce wannan sassauci na wucin gadi ne, inda ta jaddada cewa daga Hajjin 2027 za a kma tsarin biyan kuɗi ta asusun banki gaba ɗaya.

Masu ruwa da tsaki sun ce matakin zai taimaka wajen kauce wa matsaloli, yayin da ake shirin wayar da kan alhazai kan sabon tsarin kafin a fara aiwatar da shi.

‘Yan sandan Abuja sun ceto wata mata mai tabin hankali da jaririyarta

Rundunar ‘yan sandan Abuja, babban birnin tarayyar Nijeriya ta sanar da cewa a ranar 3 ga Afrilu, 2026 da misalin karfe 12:30 na dare, jami’an Rapid Response Squad da ke sintiri a yankin Kwali sun gano wata mata mai tabin hankali da mace a bakin hanya a kauyen Kwaita.

A sanarwar da SP Josephine Adeh ta aike wa DCL Hausa, ta ce jami’ansu sun kai matar da jairiryarta Asibitin Kwali inda aka ba su kulawar lafiya kafin a sallame su cikin koshin lafiya, sannan aka mika su ga jami’in jin kai na karamar hukumar Kwali, Malam Sadiq Kwali.

Babu bambanci tsakanin waɗanda ke jam’iyyar APC, PDP da kuma ADC – Farouk Adamu Aliyu

Jigo a jam’iyyar APC mai mulki a Nijeriya, Farouk Adamu Aliyu ya bayyana cewa babu bambanci tsakanin mutanen da ke jam”iyyar PDP, APC da na ADC domin tsakanin su ake fita a koma wata jam’iyyar.

A hirarsa da DCL Hausa, dan siyasar ya bayyana cewa , mutanen da ake gani a jam’iyyar ADC sune dai ‘yan APC da suka fita saboda haka basu da wani bambanci, illa kawai ‘yan Nijeriya ne ya kamata su yi alkalanci.

Farouk ya ce babu wani yunƙuri da jam’iyyar APC ke yi na murkushe ‘yan adawa, kawai su bi tsarin dokar ƙasa su zauna lafiya.

Ya kara da cewa ko a shekarar 2014, wasu Gwamnoni daga jam’iyyar PDP sukazo aka yi haɗaka da su domin fatattakar jam’iyyar, don haka APC ma a yanzu na ci gaba da yin zawarcin mutane masu amfani da za su taimaki tsarin.

Gwamnonin APC da za su kammala wa’adin mulkinsu na biyu: Shin su wanene za su gaje su?

Yayin da aka fara buga kugen siyasa ke gabanin zabukan gama gari na 2027, ana kara mai da hankali kan gwamnonin da aka zaba karkashin jam’iyyar APC wadanda ba za su sake komawa mulki ba saboda sun cinye wa’adin mulkinsu na biyu kamar yadda kundin tsarin mulkin kasar ya tanadar.

A wannan rahoto, gidan talabijin na TVC News ta hada ya yi nazari kan gwamnonin da ke dab da kammala wa’adin mulkinsu kamar yadda kundin tsarin mulki ya tanada.

Yayin da wasu daga cikinsu suka fara nuna goyon baya ga wadanda suke son su gaje su, wasu kuma na jiran umarnin shugabannin jam’iyya kafin su tsara yadda magajin zai kasance.

Babagana Umara Zulum

Farfesa Babagana Umara Zulum, shi ne Gwamnan jihar Borno, yana wa’adinsa na biyu tun daga ranar 29 ga Mayu 2023 karkashin jam’iyyar APC.
An haife shi a ranar 25 ga Agusta 1969 a karamar hukumar Mafa ta jihar Borno, inda yake da digirin B.Eng daga jami’ar Maiduguri, da M.Sc daga jami’ar Ibadan, da kuma digirin digirgir a fannin Soil and Water Engineering.
Ya yi suna a aikin gwamnati da bangaren ilimi, inda ya kai matsayin Farfesa kuma ya taba zama Rector na Ramat Polytechnic.
Gwamna Zulum ya shiga siyasa a 2015 a matsayin kwamishinan farko na sake gina yankunan da rikici ya shafa, kafin a zabe shi gwamna a 2019, sannan aka sake zabensa a 2023.

Ahmadu Umaru Fintiri

Dan siyasa ne a Nijeriya wanda a yanzu yake matsayin Gwamnan jihar Adamawa.
An haife shi a ranar 27 ga Oktoba 1967 a Gulak, karamar hukumar Madagali, inda ya yi karatun farko kafin ya samu digirin BA a Tarihi a 1992 da kuma takardar digiri na gaba a fannin manufofi da dabarun gudanarwa a 2004 daga jami’ar Maiduguri.
Fintiri ya fara siyasa a majalisar dokokin jihar Adamawa, inda ya rike mukamai daban-daban har ya zama kakakin majalisa.
A wannan lokaci, ya taba zama mukaddashin gwamna sau biyu a 2012 da 2014 bayan tsige Gwamna Murtala Nyako, wanda hakan ya kara masa kwarewa a siyasa.
An zabe shi gwamna a 2019 sannan aka sake zabensa a 2023 karkashin jam’iyyar PDP, inda ya yi fice wajen gina tituna da inganta ilimi.
A wani babban sauyin siyasa, Fintiri ya sauya sheka zuwa APC a ranar 27 ga Fabrairu 2026, yana mai cewa hakan zai taimaka wajen daidaita jihar Adamawa da manufofin gwamnatin tarayya karkashin Shugaban kasa Bola Tinubu.
An karbe shi a hukumance cikin APC a watan Maris 2026, inda aka amince da shi a matsayin jagoran jam’iyyar a jihar Adamawa.

Mai Mala Buni

Mai Mala Buni, shi ne Gwamnan jihar Yobe, yana wa’adinsa na biyu kuma na karshe tun daga ranar 29 ga Mayu 2019, bayan sake zabensa a 2023 karkashin APC.
An haife shi a ranar 19 ga Nuwamba 1967 a Buni Yadi, jihar Yobe, inda yake da digiri a fannin International Relations daga Benin Republic, da kuma digiri na biyu daga jami’ar Leeds Beckett.
Kafin siyasa, ya yi kasuwanci a bangaren noma, mai da sufuri.
Ya fara siyasa a 1991 a matsayin kansila, sannan ya rike mukamai daban-daban har ya zama babban jigo a APC a matakin kasa.
Gwamnatinsa na mayar da hankali kan farfado da yankunan da rikici ya shafa da kuma ci gaban ababen more rayuwa.

Muhammadu Inuwa Yahaya
Muhammad Inuwa Yahaya, shi ne Gwamnan jihar Gombe, yana wa’adinsa na biyu kuma na karshe tun daga ranar 29 ga Mayu 2019, bayan sake zabensa a 2023 karkashin APC.
An haife shi a ranar 9 ga Oktoba 1961 a Gombe, inda yake da digiri a Accounting daga jami’ar Ahmadu Bello, Zariya.
Ya fara aiki a bangaren gwamnati kafin ya koma kasuwanci, sannan ya taba zama kwamishinan kudi daga 2003 zuwa 2010.
Gwamnatinsa na tafiya karkashin tsarin DEVAGOM.
Kasafin kudin 2026 na Naira biliyan 617.95 ya ware kusan kashi 70 cikin 100 domin ayyukan ci gaba kamar hanyoyi, wuta, tsaro da noma.

AbdulRahman AbdulRazaq
AbdulRahman AbdulRazaq dan kasuwa ne kuma dan siyasa, yana wa’adinsa na biyu a matsayin Gwamnan jihar Kwara, kuma shi ne shugaban kungiyar gwamnonin Nijeriya (NGF).
An haife shi a ranar 5 ga Fabrairu 1960 a Zariya, jihar Kaduna, cikin gidan fitaccen lauya na farko a Arewacin Nijeriya.
Ya yi karatu a Kaduna da Ilorin, sannan ya samu horo a jami’ar Oxford da ke Ingila.
Kafin siyasa, ya yi fice a harkar mai da gas, inda ya kafa kamfanin NOPA Oil Services.
Ya shahara a siyasa bayan nasarar da ya samu a zaben 2019, inda ya kawo karshen tasirin siyasar Saraki a jihar Kwara karkashin tafiyar “Otoge”.

Babajide Sanwo-Olu
Babajide Olusola Sanwo-Olu dan siyasa ne, wanda ya zama Gwamnan jihar Lagos tun daga 29 ga Mayu 2019, kuma aka sake zabensa a 2023 karkashin APC.
An haife shi a ranar 25 ga Yuni 1965 a Lagos.
Ya yi karatu a jami’ar Lagos inda ya samu digiri da MBA, sannan ya samu karin horo daga cibiyoyi daban-daban na duniya.
Kafin siyasa, ya yi aiki a bankuna da kamfanoni masu zaman kansu.
Ya rike mukamai da dama a gwamnatin jihar Lagos kafin ya zama gwamna.
Mulkinsa na tafiya karkashin tsarin THEMES da ke mayar da hankali kan sufuri, lafiya, ilimi, tsaro da tattalin arziki.

Dapo Abiodun
Prince Dapo Abiodun, shi ne Gwamnan jihar Ogun tun daga 29 ga Mayu 2019, kuma yana wa’adinsa na biyu bayan sake zabensa a 2023 karkashin APC.
An haife shi a ranar 29 ga Mayu 1960 a Ogun.
Ya yi karatu a Amurka a fannin Accounting, sannan ya yi aiki a bangaren mai da gas.
Ya kafa kamfanoni kuma ya rike mukamai daban-daban na gwamnati.
Mulkinsa na karkashin tsarin ISEYA wanda ya hada da gine-gine, walwala, ilimi, matasa da noma.

Douye Diri
Sanata Douye Diri shi ne Gwamnan jihar Bayelsa, yana wa’adinsa na biyu.
An haife shi a ranar 4 ga Yuni 1959.
Ya fara aiki a matsayin malami kafin shiga siyasa inda ya rike mukamai da dama ciki har da dan majalisa da sanata.
Gwamnatinsa na mayar da hankali kan gine-gine, noma da tsaro.
A 2026, ya sanya hannu kan kasafin kudin Naira tiriliyan 1.01 domin ayyukan ci gaba.

Hope Uzodinma
Sanata Hope Uzodinma, shi ne Gwamnan jihar Imo, yana wa’adinsa na biyu kuma na karshe tun bayan sake zabensa a 2023.
An haife shi a ranar 12 ga Disamba 1958.
Ya yi kasuwanci a bangaren mai da gas kafin shiga siyasa, inda ya taba zama sanata.
Ya zama gwamna a 2020 bayan hukuncin kotun koli.
Mulkinsa na karkashin tsarin “3R” wanda ke nufin sake gina, gyara da farfado da jihar.

‘Sha kuruminka, duk kuri’un jihar Kaduna, naka ne – Tabbacin Tajuddeen Abbas ga Shugaba Tinubu

Shugaban Majalisar Wakilai ta Nijeriya, Hon. Tajudeen Abbas, ya bai wa Shugaban kasa, Bola Ahmed Tinubu, tabbacin cewa dukkanin yankunan majalisar dattawa uku na jihar Kaduna sun hada kai suna goyon bayansa da kuma Gwamna Uba Sani a babban zaben 2027 da ke tafe.

Abbas ya bayyana hakan ne a Fadar Shugaban kasa da ke Abuja, lokacin da ya jagoranci tawagar manyan masu ruwa da tsaki daga Kaduna, ciki har da Sanata Sunday Marshall Katung mai wakiltar Kaduna ta Kudu, da Sanata Shehu Sani wanda ya taba wakiltar Kaduna ta Tsakiya tsakanin 2015 zuwa 2019.

Ya ce ziyarar wata muhimmiyar ganawa ce domin sanar da shugaban kasar yadda jam’iyyar APC ke kara samun karbuwa a fadin jihar Kaduna.

Shugaban majalisar ya jaddada cewa jam’iyyar APC ta samu cikakkiyar karbuwa a dukkan sassan jihar, inda ya tabbatar da cewa zaben 2027 ya kusa zama tabbatacce ga jam’iyyar, tare da samun gagarumar nasara a dukkanin matakai.

A cewarsa, sabanin yadda a baya APC ke da karfi ne kawai a yankunan arewa da tsakiya, yanzu haka sabbin sauye-sauyen siyasa sun sa jam’iyyar ta samu karbuwa har a yankin kudancin jihar, wanda a baya ake dauka a matsayin sansanin PDP.

Ya kara da cewa wannan nasara ta samo asali ne sakamakon yadda Gwamna Uba Sani ke tafiyar da mulki cikin hadin kai da bai wa kowa dama, wanda hakan ya jawo goyon baya daga bangarori daban-daban na addini.

Har ila yau, Abbas ya bayyana cewa sauya sheka da wasu jiga-jigan PDP suka yi, ciki har da Sanata Katung da wasu zababbun jami’ai, ya kara karfafa matsayin APC a duk fadin jihar Kaduna.

Wike ya soki yunkurin Gwamnan Bauchi Bala na barin PDP

Kasa da sa’o’i 24 bayan gwamnan jihar Bauchi, Sanata Bala Mohammed, ya bayyana shirin sauya sheka zuwa jam’iyyar ADC, shugaban jam’iyyar APC na kasa, Farfesa Nentawe Yilwatda, tare da gwamnan Kano, Abba Kabir Yusuf, sun kai ziyara fadar gwamnatin Bauchi a ranar Laraba.

An hango shugabannin biyu na shiga fadar gwamnatin, inda suka yi wata ganawa ta sirri da Gwamna Bala Mohammed.
Bayan kammala taron, babu daya daga cikin bangarorin da ya yi wa manema labarai bayani.

Ana sa ran gwamnan zai sanar da jam’iyyar da zai koma a yau Alhamis din nan.

Wannan na zuwa ne yayin da ministan babban birnin tarayya Abuja, Nyesom Wike, ya soki gwamnan kan rashin daidaito a matsayinsa.
Majiyoyi daga fadar gwamnatin sun ce ziyarar na iya nasaba da kokarin shawo kan gwamnan ya sake tunani kan shirin komawa ADC, maimakon haka ya hade da APC.

Wannan ci gaba na zuwa ne kwana guda bayan Gwamnan Bala, wanda kuma shi ne shugaban kungiyar gwamnonin PDP, ya karbi bakuncin wata tawagar jam’iyyar ADC karkashin jagorancin tsohon sakataren gwamnatin tarayya, Babachir Lawal.

Da yake magana da manema labarai bayan taron na ranar Talata, gwamnan ya danganta shirin sauya shekar nasa da rikicin da ke ci gaba da faruwa a cikin jam’iyyar PDP, yana mai cewa kokarin sulhu bai yi nasara ba.

Ya ce, “Mun tsinci kanmu a cikin wani mawuyacin hali. Na yi duk mai yiwuwa domin tabbatar da sulhu, amma hakan bai yi nasara ba.”

A yayin da yake duba ayyukan gina hanyoyi a Abuja a ranar Laraba, Wike ya zargi Gwamnan Bala da cewa a baya ya taba kokarin yin sulhu da APC, inda ya tuna da wata tafiya da gwamnan ya kai Port Harcourt a shekarar 2022, inda ake zargin ya nemi goyon bayan Bola Tinubu, kafin daga bisani ya koma goyon bayan dan takarar PDP a zaben 2023, Atiku Abubakar.

Ya ce, “Abin kunya ne sosai. Yanzu ys fada maka magana, da safe ya sauya ta, da rana kuma sai ya fadi wani daban.”

“Bala, muna farin ciki sosai da ka bayyana wa ‘yan Nijeriya wanene kai—cewa ba ka da tsayayyiyar matsaya,” in ji Wike.

Wike ya kuma yi magana kan rikicin cikin gida na PDP, yana mai cewa jam’iyyar na nan daram duk da kalubalen shari’a da take fuskanta.
Ya soki bukatar da Gwamna Bala ya gabatar na neman mukamin sakataren jam’iyyar daga abin da ya kira matsayi mai rauni.
Ya ce, “An riga an kayar da kai, ka yi rashin nasara. Kana magana ne daga matsayi mai rauni, sannan kuma kana son neman mukamin sakataren jam’iyya? Hakan ba daidai ba ne.”

Tinubu ya nada sabon shugaban PTDF, ya sabunta wa’adin shugaban TCN

Shugaban Nijeriya Bola Ahmed Tinubu ya nada Farfesa Shu’aibu Shehu Aliyu a mukamin sabon shugaban hukumar PTDF da ke lura da rarar man fetur, tare da sabunta wa’adin mulkin Injiniya Sule Ahmed Abdulaziz a matsayin shugaban kamfanin Transmission Company of Nigeria (TCN).

A wata sanarwa da hadimin shugaban kasa kan yada labarai Bayo Onanuga ya fitar, ya ce Farfesa Aliyu ya maye gurbin Ahmed Galadima Aminu, wanda ya yi murabus domin tsayawa takarar gwamna a jihar Adamawa a zaben 2027.

Sanarwar ta kara da cewa nadin da kuma sabunta wa’adin mukaman sun fara aiki nan take, inda shugaban kasa ya bayyana cewa hakan na daga cikin kokarinsa na karfafa manyan cibiyoyin makamashi da wutar lantarki a kasar.

Kafin nadin nasa, Farfesa Aliyu shi ne shugaban Hukumar Ilimin Manya, kuma ana kallonsa a matsayin kwararren malami kuma gogaggen masanin harkar gudanarwa. Shugaban kasa na sa ran zai yi amfani da kwarewarsa wajen bunkasa PTDF, musamman a bangaren horas da ma’aikata da kirkire-kirkire a harkar mai da iskar gas.

Hakazalika, an sabunta wa’adin Injiniya Abdulaziz ne bayan tantance yadda ya jagoranci cibiyar wutar lantarki, inda aka samu ci gaba a daidaiton wutar lantarki, fadada hanyoyin rarraba lantarki, da kuma sabunta tsarin aiki, lamarin da ya kara karfafa rawar da TCN ke takawa a harkar wutar lantarki ta Nijeriya.

Shugaba Tinubu ya bukaci sabbin shugabannin biyu da su gudanar da ayyukansu cikin gaskiya, kwarewa da kishin kasa, domin cimma manufofin shirin gwamnati na Renewed Hope Agenda.