DCL Hausa Radio
f DCL HAUSA FACEBOOK
Sunday, April 19, 2026
Home Blog Page 387

Sabon tsarin karatu na makarantun firamare zai fara aiki a duk fadin kasar Nijeriya daga watan Janairun 2025 – Ministan Ilimi Farfesa Tahir Mamman

Ministan Ilimi Farfesa Tahir Mamman, ya ce sabon tsarin karatu na makarantun firamare zai fara aiki a duk fadin kasar daga watan Janairun 2025.

Da yake gabatar da jawabin sa a wani taron  masu ruwa da tsaki a Abuja a ranar Litinin,FarfesaTahir Mamman  ya bayyana cewa a sabon tsarin karatun, za a bukaci daliban da ke makarantun Firamare da na sakandare su laƙanci  akalla sana’o’i biyu.

Ya ce, yana da kyau sosai dalibai su sami damar kammala makaranta da aƙalla ƙwarewa kan ayyukan hannu biyu domin samun rayuwa mai inganci. 

Ya Kara da cewa wannan wajibi ne da ya shafi dukkan makarantu a Najeriya, na gwamnati da masu zaman kansu, kuma duk makarantu za su aiwatar da shi.

Kwankwaso da ɗarikar sa ta Kwankwasiyya barazana ce ga jam’iyyar NNPP – Shugaban tsagin jam’iyyar na kasa Dr. Gilbert Agbo

Shugaban tsagen jam’iyyar NNPP na kasa Dr. Gilbert Agbo wanda ya jagoranci gangamin adawa da Kwankwasiyya a sakatariyar jam’iyyar a Minna jihar Neja, ya ce Kwankwaso da tawagar sa ta Kwankwasiyya barazana ce ga ci gaba da wanzuwar jam’iyyar.

Da yake jawabi a wurin taron shiyyar Arewa ta tsakiya a Minna, Dr. Agbo ya jaddada cewa dakatarwar da jam’iyyar ta yiwa Kwankwaso a Legas ya kawo karshen zama mamba da hannun a jam’iyyar nan take.

Dr. Gilbert wanda shi ma ya jagoranci kona jar hular ta kungiyar Kwankwasiyya a sakatariyar jam’iyyar ta jihar a Minna, ya ce matakin ya nuna karara na ballewa daga bangaren Kwankwaso.

Dokta Agbo ya ce ana sa ran gwamna Kabir Yusuf na jihar Kano zai gurfana a gaban kwamitin ladabtarwar jam’iyyar saboda rashin bin ka’idojin jam’iyyar da kuma daukakar jam’iyyar.

Cire tallafin man fetur a Nijeriya ya taimaka wurin rage fasakwaurin sa a kan iyakokin kasar – Mele Kyari

 

Shugaban kamfanin mai na Nijeriya NNPCL Mele Kyari ya ce cire tallafin mai ya taimaka wurin rage fasakaurin sa ta kan iyakokin kasar.

kyari ya bayyana hakan ne a wata hira  da ya yi da gidan talabijin na Channels Lahadin, inda ya bayyana cewa tallafin ya haifar da rashin tazara mai yawa na farashi a tsakanin Najeriya da kasashen da ke makwabtaka da ita, lamarin da ya sa fasakwauri ya ragu sosai.

Ya bayyana cewa shekaru da dama, tallafin ya samar da dama ga masu fasa-kwaurin.

Kafin cire tallafin, Kyrari ya jaddada bambancin farashin yana da yawa, abin da a cewar sa shi ke ƙarfafa masu yin fasa kwaurin.

Super Eagles ta fãsa buga wasan neman gurbin shiga gasar cin kofin Nahiyar Afirka

Hukumar kwallon kafa ta Nijeriya ta yanke shawarar janye Super Eagles daga wasan neman gurbin shiga gasar cin kofin Nahiyar Afirka ta 2025 da za tayi da Libiya a ranar talata.

Hakan ya biyo bayan yanayi Mai cike da takaici da  tawagar ta shafe sa’o’i12 a filin jirgin saman Al-Abraq na kasar Libiya, yayin da tawagar ta makale bayan wani sauƙa na gaggawa a yammacin Lahadi.

Jaridar Punch ta rawaito cewa tawagar ta Nijeriya na kan hanyar zuwa birnin Benghazi ne domin gudanar da wasan share fage mai matukar mahimman ci, lokacin da jirgin da su ka karba haya ya samu matsala .

Lamarin da ba zato ba tsammani ya sa ‘yan wasa da jami’ai suka makale ba tare da wani taimako daga hukumar kwallon kafa ta Libiya ba, abin da ya fusata kungiyar ta NFF.

NFF  ta cigaba da cewa yan wasan sun gaji saboda haka ne sun yanke shawarar ba za su buga wasan ba.

Ya kamata ‘yan Nijeriya su koma ga Allah – Obasanjo

Tsohon shugaban Nijeriya Olusegun Obasanjo ya bukaci shugabanni da malamai da ’yan kasa da su yi wa kasar addu’a domin samun sauki, yana mai cewa halin da Nijeriya ke ciki “laifun mune”

Ya ce mun yi almubazzaranci da kyautar da Allah ya ba mu amma idan muka kaskantar da kanmu, muka roke shi zai warkar da kasarmu. 

Obasanjo ya fadi haka ne a yayin wani taro da aka yi a wata majami’a da ke Abuja a ranar Lahadi

Yana yiwuwa a kawo karshen tashin hankali ga yara – MDD

Wakiliyar Majalisar Ɗinkin Duniya ta musamman kan cin Zarafin Kananan Yara, Dokta Najat Maalla M’jid ta bayyana cewa yawan cin zarafin kananan yara a duniya na karuwa.
Wani rahoton Majalisar Ɗinkin Duniya da aka fitar a ranar 10 ga watan Oktoba, ya jaddada cewa ta hanyar yin aiki tare, jihohi za su iya kawar da wannan mummunar dabi’a.
“Bayanan da aka nuna a cikin rahoton na da ban tsoro kuma mai yiwuwa ba a yi la’akari da su ba.
“Yara sama da Miliyoyi a duniya suna fama da tashe-tashen hankula na zahiri, jima’i, aikin yara, auren yara, kaciyar mata, cin zarafin jinsi, fataucin mutane, cin zarafi, da cin zarafi ta yanar gizo.
“Bayanan da aka gabatar a cikin wannan rahoto na da ban tsoro kuma mai yiwuwa rashin fahimta ne. Batutuwa kamar aikin yara, auren yara, kaciyar mata, cin zarafin mata, fataucin mutane, cin zarafi, da cin zarafi ta yanar gizo sun yawaita” Inji Dr. Maalla M’jid.
Rahoton wanda Ofishin Wakilin musamman na Majalisar Ɗinkin Duniya kan cin Zarafin Yara ya wallafa, ya yi nazari kan ci gaban da aka samu da kuma kalubalen da suka rage tun lokacin da aka kafa ofishin shekaru goma sha biyar da suka gabata.
“Duk da haka, canji yana yiwuwa. Muna bukatar takamaiman mahalli da kuma saka hannun jari mai dorewa don daukan mafita.
“Misalai masu karfi na matakan da Jihohi suka yi – sassa masu zaman kansu, masanan ilimi, shugabannin addini, cibiyoyin kare hakkin ɗan adam, kafofin watsa labarai da kungiyoyin jama’a, sun nuna cewa za a iya cimma canjin yanayin da ya dace idan muka yi aiki tare da tsarin mulki gaba daya”.
Bugu da kari, rahoton ya jaddada cewa saka hannun jari a fannin kare lafiyar yara ba zancen kashe kudi ba ne amma wani muhimmin jari ne mai fa’ida tare da samun riba mai yawa ga rayuwar yara da makomar al’umma.
“Ya’ya ba matsala bane, babbar kadara ce da ya kamata a zuba wa jari a kanta”.
Wakiliyar ta Musamman ta jaddada cewa, karfafa hadin gwiwar bangarori daban-daban na daya daga cikin manufofin karfafa kawancen kasashen duniya sama da 40 masu neman kawo karshen cin zarafin kananan yara, wanda take jagorantar tun watan Janairun 2024.
Kaddamar da sabuwar ƙawancen hanyoyin gano hanyoyin duniya a hukumance zai gudana ne ranar taron farko na Ministocin Duniya kan kawo karshen cin zarafin yara a kasar Bogota, a ranakun 7 da 8 ga Nuwamba. Wannan taron yana nufin ya zama mai canza wasa, saboda zai zama babbar dama don haɓaka ingantaccen canji ga yara.
Dr. Maalla M’jid ta kammala da cewa “Kada mu jira wasu shekaru 15 – muyi aiki yanzu ma yara tare da yara”.

Zargin rashin samun biyan bukata a shirin inshorar lafiya a Katsina

 

Zargin coge ne dai ya mamaye muryoyin wasu ma’aikatan gwamnati a jihar Katsina da ke cikin shirin taimakekeniyar lafiya na KTCHIMA da ake rajistar inshorar lafiya ga ma’aikatan gwamnati.

Ga cikakken rahoto akan wannan bato.

Rahoton KTCHIMA

Atiku ya caccaki gwamnatin Tinubu kan karin farashin man fetur

Madugun adawa a Nijeriya, Atiku Abubakar, ya bayyana cewa rashin bin ka’ida da gwamnatin shugaba Bola Tinubu ke yi sune suka haddasa tabarbarewar tattalin arzikin Najeriya.

Atiku na mayar da martani ne kan karin farashin man fetur da kamfanin NNPC ya yi, a wani sako da ya wallafa a shafinsa na Twitter a ranar Alhamis.

Atiku ya zargi shugaba Tinubu da kauda kai ga ‘yan Nijeriya kamar yadda jaridar Punch ta ruwairo.

Kamfanin NNPC ya kara farashin man fetur daga N897 kan kowace lita zuwa N1,030 a Abuja.

Ko ku tuba ko mu aike ku zuwa ga mahaliccinku- Matawalle ya gargadi masu fallasa wa ‘yan bindiga bayanai a Nijeriya

 

Karamin Ministan Tsaro, Bello Matawalle, ya gargadi ‘yan bindiga da suka addabi kasar nan kan cewa su tuba ko kuma a aike da su zuwa ga mahaliccinsu tare da gargadin masu fallasa wa ‘yan bindiga bayanan sirri.

Ministan ya yi wannan gargadin ne a wata ziyarar aiki da ya kai kauyen Gundumi da ke kananan hukumomin Isa da Sabon Birni a jihar Sokoto a ranar Alhamis, kamar yadda jaridar Daily Trust ta ruwaito.

A wani jawabi da ya yi a wajen kaddamar da shirin “Operation Fansan Yamma” a ranar Laraba, ministan ya bukaci goyon bayan al’umma domin kawo karshen matsalar tsaro.

Majalisar Kaduna ta musanta yin kwaskwarima ga dokar zaben ƙananan hukumomi

0

 Majalisar dokokin jihar Kaduna ta yi watsi da zargin da ake mata na shirin yin gyara ga dokar zaben kananan hukumomin jihar gabanin zaben kananan hukumomin da aka shirya gudanarwa a ranar 19 ga Oktoba, 2024.

Sai dai jam’iyyar PDP a jihar ta muna damuwarta kan sahihancin zaben da ke tafe.

Atabakin shugabanta na jihar, Edward Masha, ta yi zargin cewa majalisar na kokarin gyara dokar kananan hukumomin a jihar