DCL Hausa Radio
f DCL HAUSA FACEBOOK
Friday, April 17, 2026
Home Blog Page 388

Manchester City ta buga wasannin firimiya 30 ba tare da an doke ta ba

 Kungiyar Manchester City ta buga wasannin firimiya guda 30 a jere ba tare da an doke ta ba

Nasarar na zuwa ne bayan kungiyar ta doke Fulham da ci 3-2 a filin wasanta na Etih

ad

Kuskuren Jaridar Daily Trust kan rahoton SAMOA – Abdulaziz Abdulaziz

https://drive.google.com/uc?export=view&id=1EqCwvlnycrJkkHghW16clUrkLO9z5zHV
Kuskuren Jaridar Daily Trust Da Yadda Gaskiya Ta Bayyana Game Da Yarjejeniyar Samoa
Daga Abdulaziz Abdulaziz 
A ranar Laraba da ta gabata jaridar Daily Trust ta fito da jawabin neman afuwa ga gwamnatin tarayya game da labarin da ta wallafa marar tushe kan zargin cewa akwai goyon bayan auren jinsi a cikin yarjejeniyar ƙasa da ƙasa ta Samoa da gwamnatin Bola Ahmed Tinubu ta sanyawa hannu.
Neman afuwar ya biyo bayan rahoton bincike da wani kwamiti mai zaman kansa na sa ido akan aikin jarida ya gabatar wanda ya yi zuzzurfan bincike kan ƙorafin da gwamnati ta shigar game da wancan labari da jaridar Trust ta buga ranar 4 ga watan Yuli na wannan shekarar.
Saɓanin yadda aka saba gani a baya na yadda gwamnati za ta tura jami’an tsaro su kamo ƴan jarida ko su rufe gidan jaridar da ya yi abinda ya ɓatawa gwamnati rai, gwamnatin Tinubu ta bi hanyar laluma domin binciken gaskiyar lamarin da kuma bin haƙƙin ta. Kuma manyan ƴan jarida da ƙwararru ne suka zauna suka yiwa wannan labarin karatun nutsuwa kuma suka nemi bahasi daga Daily Trust, a ƙarshe suka yanke hukuncin cewa jaridar bata da hujjar wancan ikirari don haka ta bawa gwamnatin tarayya haƙuri. Hukumar gidan jaridar ta amsa lefinta, wannan ya sa suka fitar da wancan bayani na bada haƙuri.
A jawabin neman afuwar da ta fitar, Jaridar Daily Trust ta bayyana cewa ta gamsu da binciken da kwamitin ɗa’ar aikin jarida ya gabatar. Rahoton kwamitin wanda aka fitar a ranar 23 ga watan Satumba, 2024 biyo bayan ƙorafi da gwamnatin tarayya ta shigar. Kwamitin ya gano cewa duk cikin shafuka 403 na yarjejeniyar Samoa babu inda aka yi maganar ƙasashen za su goyi baya ko kare haƙƙin masu neman jinsi a matsayin sharaɗin samun tallafi ko wani taimako daga manyan ƙasashen Duniya. Kuma babu ma inda aka yi maganar masu neman jinsi kwata-kwata a cikin yarjejeniyar.
 
Tun da farko na kaɗu da jin labarin a matsayina na ƙwararren ɗan jarida. Na yi rubutu a Social Media kan yadda aka samu raunin cika ƙa’idojin aikin jarida musamman ma rashin kafa hujja. Wannan shi ne tsokacin da zan yi ko da ba na cikin gwamnati. Magana ta gaskiya har yanzu ina mamaki ta yaya labarin ya samu wucewa duk da hanyoyin tace labarai da ake da su a ɗakin buga labarai na Jaridar.
Tun farkon fitar labarin kafafen yaɗa labarai da manyan masana aikin jarida da wasu ƙwararru da ma wasu kafafen yaɗa labarai suka fito suka nuna cewa wa ce labarin an gina shi ne bisa tubalin toka, wato dai Daily Trust ta tafka kuskure. A cikin waɗanda suka fitar irin wannan matsaya bayan sun karanta labarin da kuma bin diddigi akwai irin su Farfesa Farooq Kperogi da BBC da jaridun Premium Times da Punch da ƙungiyar lauyoyi ta Najeriya, da sauransu da dama. 
Kasancewarsa abu ne da ya shafi addininmu labarin ya sanya damuwa a zukatan mutane da dama. Babban abinda ya sa kusan kowa ya yadda da labarin shi ne ya zo daga kafar da kowa yana tunanin in dai labari ya fito daga gare ta gaskiya ne.
Labarin ya fita ranar Alhamis, kuma tada ƙurar da ya yi ya sanya hakan ya sanya mutane da dama a Arewa musamman Malamai suka yi huɗubobi masu zafi a ranar Juma’a. Banga laifinsu ba saboda labarin ya zo ne daga kafar Daily Trust da aka aminta da ita.
Bayan mutane sun fusata, wasu kuma daga ƴan adawa sun ƙara rura wutar. Wasu ƙusoshin ƴan adawa sun yi ta kiran wasu malamai suna roƙonsu kan lallai su fito su ƙalubalanci  gwamnati. Wannan ne babban babban abinda ya janyo limamanmu masu daraja suka hau mimbari a fusace da labarin da ba shi da tushe. Shugaba Tinubu da gwamnatinsa da dukkaninmu haka aka yi mana tofin ala-tsine ba tare da bin diddigin zancen ba. An zargi gwamnati da siyar da Najeriya domin ɗaga darajar masu neman jinsi, da dai sauran kalamai marasa daɗi da aka yi a cikin fushi. 
Mun sha takaici ƙwarai ganin yadda duk ƙoƙarin nuna gaskiyar abin mutane da dama suka toshe kunnuwansu. Na sha tambayar mutane ko sun san cewa ba inda wannan yarjejeniyar ta sauya dokokin mu da suka haramta auren jinsi? Kuma ta yaya sanya hannu a dokar ya bawa masu auren jinsi wani ƴanci? Ba wanda zai baka amsar wannan tambayoyi, sai dai kame-kame, saboda kawai yarda da wancan rahoton na ƙarya. 
Wannan abin da ya faru babbar fadakarwa ce ga nauyin da yake kan ƴan jarida na tabbatar da hujja da tantance gaskiya. Illar da rashin yin hakan zai iya jawowa ba ƙarama ba ce domin kuwa kamar masu iya magana ke cewa, ita magana zarar bunu ce; matuƙar ta fita mayar da ita abu ne mawuyaci. 
Aikin jarida aiki ne da ke buƙatar lura da taka-tsantsan da tafiya bisa hujja. A lokacin da yake ƙaddamar da kamfanin Sardauna da yake ƙaddamar da tawagar jaridar Najeriya yayi musu gargaɗi da cewa “ku faɗi gaskiya a kan mu, kuma ku faɗa mana gaskiya akan wasu”. Ba abin da muke buƙata fiye haka.
Abdulaziz, babban mataimaki na musamman ne ga shugaban ƙasa kan yaɗa labarai.

Za mu ci gaba da saka wa malaman makaranta tun a duniya in ji Gwamnan jihar Katsina Dikko Radda

Gwamnan jihar Katsina Dr Dikko Umaru Radda ya ce gwamnatinsa za ta saka wa malamai tun a Duniya

Gwamna Radda ya bayyana hakan ne yayin mika sakon taya murna ga daukacin malamai na jihar Katsina bisa bikin ranar malamai ta duniya 2024.

‘Yan sanda a Katsina sun musanta labarin tarwatsa masu sallar Juma’a a kauyen jihar

A cikin wata sanarwa da kakakin rundunar ‘yan sandan jihar Sadiq Aliyu Abubakar ya fitar, ta ce labarin ba gaskiya bane, an kirkiro shi ne domin a jefa tsoro da razani a zukatan al’umma.
Sanarwar ta ce yadda lamarin ya faru shi ne, wasu barayin daji dauke da muggan makamai ciki hada bindiga samfurin AK-47 suka yi yunkurin kai farmaki ga wadansu manoma da ke kokarin girbe amfanin gonakinsu, amma ‘yan sanda da sojoji da jami’an sa kai na Community Watch Corp suka yi taron dangi suka tarwatsa wadannan barayin daji.
Jaridar Punch da yammacin Juma’ar nan, ta rawaito cewa ‘yan bindiga sun far wa wasu mutane da ke sallar Juma’a a kauyen Dan’Ali na karamar hukumar Danmusa ta jihar Katsina.
Sai dai jaridar ba ta ba da cikakken bayanin ko mutane nawa ne suka jikkata ko aka kashe a yayin harin ba.

Yadda wata tsohuwa ke “mining” a Abuja

 

Ibrahim Danlami, mataimakin babban manaja a wani babban kamfani mai zaman kansa a Abuja, ya dauko mahaifiyarsa da ta zo garin domin su zauna tare da jikokinta, a kan hanyarsu ta zuwa gida sai ya lura da cewa ta shagaltu da ‘mining’ ba kama hannun yaro kamar yadda Daily Trust ta ruwaito

Gwamna Zulum na jihar Borno na neman majalisa ta sahale masa karin N61b a kasafin kudin cike gibi na shekarar 2024

Babagana Umara Zulum

Gwamnan jihar Borno, Babagana Umara Zulum, ya bukaci majalisar dokokin jihar da ta sahale masa karin biliyan 61 akan kasafin farko kudin na N358.7b na shekarar 2024,domin cike gibi da gudanar da wasu ayyuka.

Kakakin majalisar dokokin jihar, Abdulkarim Lawan ne ya karanta wasikar gwamnan a zauren majalisar a yau

Ƙarin kasafin kudin dai zai shafi muhimman ayyuka da suka lalace sakamakon ambaliyar ruwa da aka yi a ranar 10 ga watan Satumba, wadda ta shafi kusan mutane miliyan 2 tare da lalata wasu sassan Maiduguri da ƙananan hukumomin da ke kewaye da ita.

Kasafin zai kuma kunshi kudaden da  gwamnati ke kashewa wajen bayar da agajin gaggawa, tallafawa manoma, farfado da tattalin arziki da kuma kula da muhalli.

A ranar Alhamis ne Gwamna Zulum ya zagaya domin tantance wurare, hanyoyi,da asibitocin da suka lalace sakamakon ambaliyar ruwan domin tantance su.

Gwamnatin jihar Borno ta sanar da bullar cutar kwalara a jihar

Gwamnan jihar Borno/Baba Gama Umarar Zulum

Kwamishinan Lafiya da ayyukan al’umma,na jihar Farfesa Baba Gana ya bayyana hakan a cibiyar kula da ido da ke Maiduguri, ya ce daga cikin samfura dari biyu da aka aika domin yin gwaji, goma sha bakwai sun kamu.

A cewarsa bullar cutar ta samo asali ne sakamakon ambaliyar ruwa da aka yi kwanakin baya a sassan jihar.

Farfesan ya ce wuraren da aka samu bullar cutar sun hada da Jere, Mafa, Konduga da kuma Dikwa.

A cewar sa haryanzu ba a samu rahoton mace-mace ba, kwamishinan ya ce ana samun karuwar masu kamuwa da cutar kwalarar a kananan hukumomin da dama, musamman ma a lokacin da jihohin Adamawa da Yobe da ke makwabtaka da ita cutar ta bulla.

Ya ce an samu rahoton mutum 451 da ake zargin sun fito ne daga kananan hukumomi daban-daban amma 17 ne aka tabbatar sun kamu da cutar.

Don haka gwamnatin jihar ta ba da sanarwar daukar matakin gaggawa don shawo kan barkewar cutar, yayin da hukumomin jin kai kamar hukumar lafiya ta Duniya WHO da Médecins Sans Frontières MSF suka samar da kayayyakin shawo kan matsalar, kuma an samar da alluran rigakafi kusan 400,000.

Bankin Duniya ya amince ya bai wa Nijeriya rancen dala miliyan 500

Hoto/Bankin Duniya

Bankin Duniya ya amince da rancen dala miliyan 500 don tallafa wa aikin da ake yi na samar da wutar lantarki mai dorewa ga Nijeriya, SPIN, da nufin rage kalubalen da ke addabar aikin.

Daraktan Bankin Duniya dake kula da samar da ababen more rayuwa na Yammaci da Tsakiyar Afirka,Chakib Jenane,ya bayyana hakan yayin wata ziyara da ya kai wa ministan albarkatun ruwa da tsaftar muhalli a Abuja ranar Alhamis.

Mista Jenane ya ce an amince da aikin ne a yayin taron da bankin duniya ya yi a ranar 26 ga watan Satumba, inda ya kara da cewa an shirya fara aikin ne a watan Janairun 2025.

A cewarsa, an tsara yin aikin ne domin magance matsalolin da suka shafi yanayi, da suka hada da ambaliyar ruwa ta hanyar amfani da shi wajen aiwatar da aikin , ya ce aikin zai amfanar da kusan mutane 950,000 da suka hada da manoma da makiya ya.

Jenane ya jaddada bukatar Nijeriya ta ci gaba da shirye-shiryen cika sharudan da suka rage domin fara aikin a watan janairu na shekarar 2025.

‘Yan Nijeriya sun gaji da halin matsin rayuwa – Kwankwaso

Sanata Rabiu Musa Kwankwaso

Tsohon dan takarar shugaban Kasa a jam’iyyar NNPP, Sanata Rabi’u Kwankwaso, ya ce da halin matsi da ake ciki a Nijeriya, ‘yan kasar za su yunkuro don kawo sauyi a 2027.

Kwankwaso ya bayyana haka ne a lokacin da ya karbi ‘ya’yan jam’iyyar APC da suka sauya sheka zuwa jam’iyyar NNPP a jihar Kano.

Kwankwaso ya tarbi ‘yan jam’iyyar APC da suka sauya sheka daga kananan hukumomin Dala, Kiru da Gwale a gidansa da ke Miller Road a Kano.

Ya ce ‘yan Nijeriya musamman ’yan Arewa sun sha wahala sosai a wannan lokacin kuma babu wani da zai tsorata su da zai sa su canja ra’ayinsu.

A cewar sa ya kamata ‘yan Nijeriya su sake tunani, yanzu ta bayyana a fili cewa al’umma na shan wahala a gwamnatin APC kuma ba za su gyara ba.

Ya kara da cewa ko da shirin su na amfani da jami’an tsaro da INEC a zabe mai zuwa, hakan ba zai yiwu ba saboda ‘yan Nijeriya sun gaji kuma tabbas za su yi fafutukar kawo sauyi.

Kotu ta umurci tsohon gwamnan Kogi Yahaya Bello da ya gurfana a gaban ta

Yahaya Bellon/Tsohon gwamnan jihar Kogi.

Wata babbar kotun tarayya da ke Maitama ta yi sammaci ga tsohon gwamnan Jihar Kogi, Yahaya Bello, inda ta umarce shi da ya gurfana a gaban ta a ranar 24 ga Oktoba, 2024.

Ana tuhumar Yahaya Bello ne tare da wasu mutane biyu Umar Oricha da Abdulsalami Hudu a bisa wasu sabbin tuhume tuhume guda 16 da hukumar yaki da yi wa tattalin arzikin Kasa zagon kasa ta EFCC ta kai gaban ta.

A baya dai wata kotun karkashin mai shari’a Emeka Nwite na babbar kotun tarayya da ke Abuja ya bayar da sammacin kama shi a ranar 17 ga watan Afrilu.

Yahaya Bello na fuskantar tuhume tuhume 19 da suka shafi karkatar da kudade da kuma karkatar da naira biliyan 80.2 a gaban kotun mai shari’a Nwite amma ya kasa gurfana a gaban ta.

Mai shari’a Maryanne Anenih, wacce aka shigar da sabbin tuhume tuhumen a gabanta, ta yanke hukunci a ranar Alhamis dinnan cewa, dole ne tsohon gwaman ya gurfana a gaban kotu domin ya kare kansa kan tuhume tuhumen da ake masa.

Sammacin ya biyo bayan bukatar da hukumar EFCC ta shigar gaban ta,hukumar dai ta yi ikirarin cewa Yahaya da wadan da ake tuhuma sun karkatar da kudaden da aka damka musu.

A hukuncin da ta yanke, Mai shari’a Anenih ta umurci hukumar EFCC da ta buga sammacin a cikin wata jarida da ke yaduwa da kuma manna kwafin sammacin a wuraren da ake gani iya gani.