DCL Hausa Radio
Friday, April 10, 2026
Home Blog Page 75

Kungiyar dattawan Arewacin Nijeriya ta bukaci a gaggauta janye yarjejeniyar hukumar haraji ta Nijeriya da kasar Faransa

0

Kungiyar dattawan Arewa ta bukaci gwamnatin Nijeriya da ta gaggauta soke yarjejeniyar fahimta da Hukumar Tara Haraji ta Nijeriya (FIRS) ta kulla da hukumar haraji ta Faransa,, tana mai cewa yarjejeniyar na barazana ga ikon tattalin arziki da tsaron kasa.

A wata budaddiyar wasika da ta aikewa gwamnatin Nijeriya, majalisar dattawa da majalisar wakilai, kungiyar ta bayyana yarjejeniyar a matsayin “hadari ga bayanan haraji,” wadda za ta iya bai wa wata kasa ikon mallakar muhimman bayanan tattalin arzikin Nijeriya.

Wasikar wadda mai magana da yawun kungiyar, Farfesa Abubakar Jiddere ya sanya wa hannu, ta ce yarjejeniyar ta wuce hadin gwiwar fasaha kawai, tana mai gargadin cewa tana zama wata hanya kai tsaye da ba ta da kariya zuwa cibiyar tsarin haraji na Nijeriya, tare da mika bayanai masu matukar muhimmanci ga ikon wata kasa ta waje.

SERAP na barazanar gurfanar da ministan shari’a na Nijeriya kan kin aiwatar da hukuncin kotu game da badakalar N6trn na hukumar NDDC

0

Kungiyar kare hakkin dan-adam da tabbatar da gaskiya (SERAP) ta yi barazanar shigar da kara kan Ministan Shari’a da babban Lauyan Nijeriya, Mista Lateef Fagbemi, SAN, saboda rashin aiwatar da hukuncin kotu kan zargin almundahana na Naira tiriliyan 6 da ake tuhumar Hukumar Ci Gaban Niger Delta (NDDC) da yi.

A cikin wata wasika da aka sanya ranar 13 ga Disamba, kungiyar ta umurci Fagbemi da ya aiwatar da hukuncin da Alh. Justice Gladys Olotu ta bayar a ranar 10 ga Nuwamba, 2025.

Kotun ta umurci Fagbemi da Shugaba Bola Tinubu da su “fitar da sunayen wadanda ake zargi da almundahana a cikin Naira tiriliyan 6 da aka ware don aiwatar da ayyuka 13,777 da aka dakatar da su da kuma gudanar da NDDC tsakanin 2000 da 2019.”

Hukuncin ya kuma umarci wallafa “rahoton binciken kudi na NDDC da aka mika ga gwamnatin tarayya a ranar 2 ga Satumba, 2021.” SERAP ta bayyana cewa rashin aiwatar da hukuncin wulakanci ne ga tsarin shari’a da doka a kasar.

Kungiyar ta gargadi cewa ci-gaba da kin aiwatar da hukuncin na iya sanya Fagbemi da Shugaba Tinubu fuskantar daukar alhakin kansu.

An fara taro shugabannin kasashen ECOWAS a Abuja

0

An kaddamar da zama na 68 na shugabannin kasashen ECOWAS a cibiyar taro ta fadar gwamnatin Nijeriya, Abuja, ranar Lahadi.

Taron zai mayar da hankali kan musayar ra’ayi na musamman kan makomar kungiyar, da tattaunawa kan muhimman batutuwa na yankin, ciki har da zaman lafiya a siyasa, hadin kai a tsaro, da hade-haden tattalin arziki.

Shugabannin yankin sun isa Nijeriya kafin taron, wanda Shugaban Sierra Leone kuma Shugaban ECOWAS, Julius Maada Bio, ke jagoranta.

A cewar sanarwa a shafinsa na X, Bio ya isa Abuja ranar Asabar don jagorantar zaman, inda ya ce yana fatan tattaunawa mai ma’ana kan kalubalen gaggawa da yankin ke fuskanta, musamman abubuwan da suka shafi Guinea-Bissau da Benin.

Jam’iyyar ADC ta fara rajista da tantance mambobi na kwanaki 90 a fadin Nijeriya

0

Jam’iyyar African Democratic Congress (ADC) ta fara shirin rajista, tantancewa da kuma jawo sabbin mambobi na tsawon kwanaki 90 a fadin Nijeriya, domin karfafa jam’iyyar daga tushe.

Jam’iyyar ta bayyana hakan ne a cikin wata sanarwa da sakataren yada labaranta na kasa, Malam Bolaji Abdullahi, ya fitar a ranar Asabar, inda ya ce an dauki matakin ne bayan kammala taron kwamitin gudanarwa na kasa da aka gudanar a ranar 27 ga watan Nuwamba, 2025, bisa tanadin kundin tsarin jam’iyyar.

ADC ta kuma sanar da shirinta na gudanar da tarukan zabe a matakin rumfunan zabe, mazabu da kananan hukumomi daga ranar 20 zuwa 27 ga Janairu, 2026, kafin babban taron kasa da aka shirya gudanarwa a watan Fabrairu, 2026 a Abuja.

Jam’iyyar ta ce wannan shiri na da matukar muhimmanci wajen karfafa hadin kan mambobi da tsari a fadin kasa.

Ya kamata a haramta amfani da kafafen sada zumunta ga ’yan kasa da shekara 16 a Nijeriya – Femi Falana

0

Babban lauya kuma SAN, Femi Falana, ya bukaci a haramta amfani da kafafen sada zumunta ga yara ’yan kasa da shekara 16 a Nijeriya, yana mai cewa hakan na da muhimmanci domin kare lafiyar tunani da tarbiyyar yara.

Falana ya bayyana hakan ne a ranar Asabar a Lagos, yayin bikin kaddamar da gasar Dare2Debate, inda ya ce kasashe da dama a duniya sun fara daukar irin wannan mataki, yana mai ambaton Ostiraliya da ta haramta wa yara ’yan kasa da shekara 16 shiga kafafen sada zumunta.

Ya kara da cewa dole ne Nijeriya ta bi wannan hanya domin amfanin yara, yana mai cewa dole a tsara ka’idoji da dokoki da za su daidaita amfani da kafafen zamani, saboda tasirin da suke da shi kan rayuwar matasa da makomar al’umma.

Ba zan koma APC ba, duk kuwa da bibiyata da fadar shugaban kasa ke yi – Sanata Natasha

0

Sanatar Kogi ta Tsakiya, Natasha Akpoti-Uduaghan, ta ce ba ta da niyyar ficewa daga jam’iyyar PDP zuwa APC, duk da cewa ana ta yi mata tayin sauya sheka daga wasu mutane da ke da alaka da fadar shugaban kasa da kuma wasu ’yan majalisa.

Ta bayyana hakan ne a wata hira da ta yi a shirin Mic On Podcast, inda ta ce ko da rikicin da ke addabar PDP ya tsananta, ba za ta bi sahun masu sauya jam’iyya ba, tana mai cewa ba ta yarda da barazana ko rarrashi na siyasa.

Sanatar ta kara da cewa an sha tuntubarta a lokuta daban-daban, har da kwanan nan, amma ta fi son ci-gaba da zama a PDP, tana mai cewa har yanzu tana tattaunawa kan makomarta ta siyasa, ciki har da yiwuwar sake tsayawa takara, amma ba a yanke hukunci ba tukuna.

Hukumar EFCC ta gargadi ‘yan Nijeriya kan girmama masu cin hanci da rashawa

0

Hukumar EFCC ta bukaci ’yan Nijeriya da su daina yabawa ko girmama mutanen da aka samu da laifin cin hanci da rashawa, tana mai cewa hakan na raunana yaki da almundahana a kasar.

Shugaban sashen shari’a na EFCC reshen Kaduna, Nasir Salele, ya ce abin takaici ne yadda al’umma ke kare wadanda aka yanke wa hukunci, har ma a wasu lokuta su tarbe su da shagali ko ba su sarautar gargajiya bayan fitowa daga gidan yari.

EFCC ta jaddada cewa yaki da cin hanci ba aikin hukuma kadai ba ne, tana kuma kira ga kafafen yada labarai da jama’a su taimaka wajen wayar da kan al’umma da kin amincewa da cin hanci da rashawa.

John Cena ya yi ritaya daga “wrestling” bayan shafe shekaru 24 yana jan zarensa

0

Fitaccen gwarzon kokawar “Wrestling”, John Cena, ya yi ritaya bayan wasan bankwana da ya yi a Capital One Arena da ke Washington DC. Cena ya fuskanci Gunther a gasar Saturday Night’s Main Event, inda aka tilasta masa mika wuya bayan rike shi da sleeper hold, lamarin da ya jefa magoya baya cikin alhini.

Wasan ya dauki kusan mintuna 25, kuma shi ne karo na farko da John Cena ya taba mika wuya a tarihin kokawarsa. Bayan kararrawa ta buga, ‘yan kokawa daga dakin ‘yan wasa sun fito domin girmama shi, yayin da Cena ya bar abin hannunsa da takalmansa a cikin zobe, alamar yin ritaya, kafin ya yi bankwana da magoya baya.

John Cena na barin “wrestling” a matsayin gwarzo sau 17 na duniya, wanda shi ne mafi yawa a tarihin wasan. Ya fara kokawa a 2002, ya shahara da taken “You Can’t See Me”, sannan daga baya ya yi fice a fina-finai. Masana da magoya baya na kallonsa a matsayin daya daga cikin mafi girman ‘yan kokawa da WWE ta taba samu.

Gwamnatin jihar Bayelsa ta umurci binciken gawar mataimakin gwamnnan domin gano musabbabin mutuwar fuju’arsa

0

Gwamnan Jihar Bayelsa, Sanata Douye Diri, ya bayar da umarnin a gudanar da bincike (autopsy) kan gawar marigayi mataimakinsa, Sanata Lawrence Ewhrudjakpo, domin gano ainihin musabbabin mutuwarsa.

Gwamna Diri ya bayyana hakan ne a ranar Asabar yayin da tsohon Shugaban Nijeriya, Dr Goodluck Jonathan, ya kai masa ziyarar ta’aziyya a fadar gwamnati da ke Yenagoa.

Diri ya ce umarnin ya zama dole ne sakamakon jita-jita da ke yawo a kafafen sada zumunta game da mutuwar mataimakin gwamnan kamar yadda jaridar Punch ta ruwaito.

A nasa bangaren, Jonathan ya bayyana mutuwar Ewhrudjakpo a matsayin babban rashi ga al’ummar Bayelsa, yana mai cewa marigayin ya kasance mutum mai himma da aminci, wanda ya wakilci gwamnan jihar a shirye-shiryen Gidauniyar Jonathan, ciki har da taron Democracy Dialogue da aka gudanar a Benin, Jihar Edo.

Shugaba Tinubu da APC sun shirya samu dimbin kuri’u a Kudu da Arewa ta Tsakiya a zaben 2027

0

Jam’iyyar APC na tsara wata sabuwar dabara domin tabbatar wa Shugaba Bola Tinubu nasara a zaɓen 2027, ta hanyar ƙarfafa goyon baya a yankunan Kudu da Arewa ta Tsakiya, a daidai lokacin da wasu ƙungiyoyi a Arewa ke nuna rashin gamsuwa da gwamnatinsa.

Jaridar Punch ta ruwaito cewa, majiyoyi a cikin jam’iyyar sun ce an fara wannan shiri tun sama da watanni biyar da suka wuce, bayan rahotanni sun nuna yiyuwar turjiya daga wasu sassan Arewa da kuma haɗin gwiwar ’yan adawa. Sun ce manyan jiga-jigan APC ne ke jagorantar dabarar, da nufin kakkabe barazanar siyasa tun kafin 2027.

A cewar majiyar, APC na da niyyar tabbatar da cewa dukkan jihohin Kudu sun tsaya tsayin daka tare da Tinubu, tare da jingina da muhimmancin ƙuri’un Arewa ta Tsakiya, domin rage tasirin duk wata adawa da ka iya tasowa daga Arewa.