Sunday, April 5, 2026
HomeLabaraiMalami ya musanta zargin daukar nauyin ta’addanci

Malami ya musanta zargin daukar nauyin ta’addanci

Tsohon Babban Lauyan Nijeriya, Abubakar Malami (SAN), ya musanta zarge-zargen da ke danganta shi da daukar nauyin ta’addanci, yana mai cewa zargin ba su da tushe kuma siyasa ce kawai ake yi da sunansa.

A wata sanarwa da ya fitar ranar Juma’a, Malami ya ce hankalinsa ya kai kan wani rubutu da ke nuni da cewa shi da wasu mutane suna da alaka da wadanda ake zargi da ta’addanci ko taimaka wa masu aikata laifin.

Jaridar Punch ta ruwaito cewa tsohon ministan ya bayyana wadannan zarge-zarge a matsayin “ba su da tushe, balle makama.”

Ya ce ba a taba gayyatar sa, bincike ko kuma tuhumarsa ta kowace hanya daga wata hukuma ta tsaro a cikin gida ko waje ba kan batun daukar nauyin ta’addanci.

Malami ya jaddada cewa irin wadannan rahotanni na iya bata suna da tayar da hankali, don haka akwai bukatar a yi taka-tsantsan wajen yada bayanai marasa inganci.

Ukashatu Ibrahim Wakili
Ukashatu Ibrahim Wakilihttps://dclhausa.com
Ukashatu Wakili, Mataimakin Manajan Edita kuma Mai Kula da Shirin Koyon Sanin Makamar Aiki ne a DCL Hausa. A matsayinsa na ƙwararren ɗan jarida yana tsara ayyukan rediyo da kafafen sada zumunta, fassarar labarai, da tabbatar da sahihancin bayanai. Yana jagorantar shirin horaswa ga masu koyon aiki tare da kula da ingancin rubuce-rubuce da shirye-shiryen gidan jaridar.
RELATED ARTICLES

LEAVE A REPLY

Please enter your comment!
Please enter your name here

Most Popular

Recent Comments

Mustapha madu bande on Tarihin marigayi Aminu Dantata