DCL Hausa Radio
Kaitsaye

Kwace mulki daga hannun Abba gida-gida ka iya tayar da rikicin da zai mamaye Africa- NNPP

-

 Shugabancin jam’iyyar
NNPP ya yi gargadin cewa amfani da karfin iko wajen kwace nasarar da Abba Kabir
Yusuf ya samu a jihar Kano, ka iya tayar da hankali, wanda zai iya mamaye
Najeriya har ma ya tsallaka zuwa wasu kasashen Africa.

Google search engine

 

Ta cikin wata
sanarwa da mai rikon kwaryar shugabancin jam’iyyar Abba Kawu Ali ya sanyawa hannu
aka kuma rabawa Kungiyar kasashen yammacin Africa, da ofishin jakadancin
Kungiyar tarayyar turai da na kasar Amurka da Burtaniya, ta ce akwai manyan
alamu da ke nuna cewa jam’iyyar APC ta lashi takobin yin duk mai yiwuwa wajen
kawace mulkin duk da bata yi nasara ba.

Sanarwar ta ce idan
aka lura da yadda jihar Kano ke ciki, ana zaman dar-dar ne, saboda yadda jama’ar
da suka fita kwan su da kwarkwata suka zabi Abba, amma ake shirin kwace wa,
wanda matukar hakan ta tabbata shakka babu zasu iya tayar da rikici.

Sanarwar ta kuma kara
da cewa akwai hasashen cewa jama’ar Kano ba zasu yi hakuri irin wanda suka yi a
2019 ba lokacin da aka yi amfani da wasu dokoki wajen kwace mulki kiri-kiri.

Abba Kawu Ali, ya
kuma ce akwai bukatar wadannan hukumomi da kasashen duniya su sanya idanu kan
wannan shari’a su kuma tabbatar an yi gaskiya, matukar ba haka ba kuma akwai
yiwuwar jama’a su dauki doka a hannun su.

LEAVE A REPLY

Please enter your comment!
Please enter your name here

Sabbin Labarai

INEC za ta fara sabuwar rijistar katin zaɓe daga ranar 18 ga Agusta a Nijeriya

Hukumar Zaɓen Nijeriya INEC ta sanar da ranar 18 ga watan Agusta, 2025 a matsayin ranar da za ta fara sabuwar rijistar katin zaɓe a...

Kamfanin NNPCL ya musanta labarin cefanar da matatar man birnin Port Harcourt

Kamfanin man fetur na Nijeriya NNPCL ya musanta labarin cefanar da matatar mai ta Fatakwal ga yan kasuwa A Yayin wani taro da kamfanin ya gabatar...

Mafi Shahara