DCL Hausa Radio
Kaitsaye

Mu tunkari matsalolin mu kada mubari sufi karfin mu-sarkin musulmi

-

Mu tunkari matsalolin mu kada mubari sufi karfin mu-sarkin musulmi

Maimartaba Sarkin Musulmi, Alhaji Muhammadu Sa’ad Abubakar, ya shawarci ‘yan Nijeriya da su amince da kalubalen da suke fuskanta, su kuma yi kokarin magance su.

Google search engine

Sarkin ya bayyana haka ne yayin da yake karbar bakuncin ministan tsaro, Muhammad Badaru Abubakar a fadarsa a ranar Juma’a, sarkin yace bai kamata mubari wasu suyi nasara a kan mu ba,domin idan babu tsaro, ba za mu iya samun komai ba.

Ya ce ministan tsaro ya san nauyin da Allah ya dora masa,kuma ya yi imanin yana tuntuɓar masu ruwa da tsaki don taimaka masa wajen yaki da matsalar tsaro a fadin kasar nan.

Akwai kalu bale, amma masu ruwa da tsaki koda yaushe suna tuntubar juna domin samun mafita a al’amura da dama da suka shafi harkokin tsaro.

Sarkin Musulmi ya bada tabbacin cewa sarakunan gargajiya za su yi duk mai yiwuwa don ganin an samu zaman lafiya da kwanciyar hankali a kasar nan.

Sai dai ya yi kira da a ci gaba da tallafa wa jami’an tsaron da su ka sadaukar da rayuwarsu domin zaman lafiya a kasar nan.

LEAVE A REPLY

Please enter your comment!
Please enter your name here

Sabbin Labarai

INEC za ta fara sabuwar rijistar katin zaɓe daga ranar 18 ga Agusta a Nijeriya

Hukumar Zaɓen Nijeriya INEC ta sanar da ranar 18 ga watan Agusta, 2025 a matsayin ranar da za ta fara sabuwar rijistar katin zaɓe a...

Kamfanin NNPCL ya musanta labarin cefanar da matatar man birnin Port Harcourt

Kamfanin man fetur na Nijeriya NNPCL ya musanta labarin cefanar da matatar mai ta Fatakwal ga yan kasuwa A Yayin wani taro da kamfanin ya gabatar...

Mafi Shahara