DCL Hausa Radio
Kaitsaye

Sanatocin Arewacin Nijeriya sun yaba wa Shugaba Tinubu kan umarnin sakin kananan yara da aka gurfanar saboda zanga-zangar#BadGovernance

-

Shugaba Tinubu

Sanatoci daga yankin Arewa sun yabawa Shugaban kasa Bola Ahmed Tinubu bisa bayar da umarnin sakin kananan yara da ake tsare da su a lokacin zanga-zangar #BadBadGovernance.

Google search engine

Sanatocin karkashin kungiyar Sanatocin Arewa, a wata sanarwa mai dauke da sa hannun shugabanta, Abdulaziz Musa Yar’adua, a ranar Litinin, sun ce shawarar da Tinubu ya yanke ya nuna aniyarsa ta kare hakki da walwalar matasan Nijeriya.

Ya ce bisa umarnin da shugaban ya bayar ga babban lauyan gwamnatin tarayya, Lateef Fagbemi, da a gaggauta sakin mutanen, wannan wani abin farin ciki ne, kuma sun nuna godiya da jagorancin shugaban kasa wajen magance wannan matsala.

A cewar sanarwar an kuma yaba da kokarin shugabannin Arewa da suka yi namijin kokari wajen ganin an sako wadannan yara kanana.Jajircewarsu da bayar da shawarwari sun taimaka wajen kawo karshen wannan al’amari gaba daya.           

Ya kuma yi kira ga shugabannin Arewa da su ba da fifiko kan tsaro da ilimin yara,ya ce yana da mahimmanci a samar da yanayi mai kyau da matasa za su girma da bunƙasar tattalin arziki tare da ilimi ba tare da cin zarafi ba.

  

LEAVE A REPLY

Please enter your comment!
Please enter your name here

Sabbin Labarai

Dalori ya karbi ragamar jagorancin jam’iyyar APC a hukumance

Shugaban riko na jam’iyyar APC, Ali Bukar Dalori, ya bukaci shugabanni da mambobin jam’iyyar da su zauna cikin hadin kai bayan murabus din tsohon shugaban...

An dakatar da jirgin Rano Air kan zargin matsalar inji – NCAA

Hukumar kula da sufurin jiragen sama ta Najeriya (NCAA) ta dakatar da wani jirgin Rano Air mai lamba 5N-BZY bayan fuskantar hatsarin gobara da matsalar...

Mafi Shahara