DCL Hausa Radio
Kaitsaye

APC ta lashe zaben Gwamnan jihar Ondo

-

Hukumar zabe a Nijeriya ta bayyana gwamna Lucky Aiyedatiwa a matsayin wanda ya lashe zaben gwamnan jihar Ondo da kuri’u 366,781.

Shi kuwa ‘dan takarar jami’iyyar PDP kuma tsohon mataimakin gwamna Agboola Ajayi ya samu kuri’u 117,845.
Jam’iyyar Labour Party da ta samu kuri’u 1,162 kamar yadda RFI Hausa ta rawaito.
Shugaban jami’ar gwamnatin tarayya dake Lokoja kuma baturen zaben Farfesa Olayemi Akinwunmi ne ya gabatar da sakamakon zaben a gaban ‘yan jarida bayan kammala tattara alkaluman kananan hukumomi 18 wadanda aka tabbatar da nasarar Aiyedatuwa a cikin su baki daya.

LEAVE A REPLY

Please enter your comment!
Please enter your name here

Sabbin Labarai

Hukumomin mulkin sojan Nijar sun kama wasu ‘yan jarida uku na Radio Sahara da ke jihar Agadez

Rahotanni daga gidan Radio Sahara Fm da ke jihar Agadez sun tabbatar da kama wasu 'yan jaridar gidan radiyon guda uku da suka hada da...

Majalisar wakilan Nijeriya ta ba gwamnonin Benue da Zamfara da shugabannin majalisunsu su wa’adin mako daya su gaggauta bayyana a gaban kwamitinta

Majalisar wakilan Nijeriya ta ba gwamnan jihar Benue, Hyacinth Alia, da na jihar Zamfara, Dauda Lawal, tare da shugabannin majalisun dokokin jihunsu wa’adin mako guda...

Mafi Shahara