DCL Hausa Radio
Kaitsaye

An sake fasalta masu magana da yawun Shugaba Tinubu

-

 

Google search engine

Sunday Dare, Daniel Bwala da Bayo Onanuga su ne masu magana da yawun shugaban kasa – fadar gwamnatin Nijeriya. 

Shugaban Nijeriya Bola Ahmad Tinubu ya sake nada mukamai guda biyu na mutanen da za su rika magana da yawun fadar shugaban kasa. 

Wata sanarwa da Hadimin shugaban ƙasa kan yaɗa labarai Bayo Onanuga ya fitar, ta ce yanzu ba mutum daya ne zai riƙa magana da yawun shugaban ba. 

Ko baya ga shi Bayo Onanuga, shugaba Tinubu ya amince da naɗa Mista Sunday Dare da kuma Daniel Bwala a matsayin masu ba shi shawara akan yada labarai da harkokin sadarwa. 

Wannan dai wani mataki ne da ake kallo garambawul da gwamnatin ke yi, a cewar jaridar Premium Times.

LEAVE A REPLY

Please enter your comment!
Please enter your name here

Sabbin Labarai

Buhari mutum ne mai girmama al’adu da masarautu – Sarkin Musulmi

Sarkin Musulmi, Alhaji Muhammad Sa’ad Abubakar, ya shiga sahun wadanda ke jimamin rasuwar tsohon Shugaban Najeriya, Muhammadu Buhari, wanda ya rasu a wani asibiti a...

An rufe ofishin jakadancin Amurka na Abuja da Legas don jimamin rasuwat Buhari

Ofishin jakadancin Amurka da ke Abuja da kuma na Legas za su kasance a rufe a ranar Talata, 15 ga Yuli, 2025, domin girmamawa da...

Mafi Shahara