DCL Hausa Radio
Kaitsaye

Majalisar dattawa ta amince da bukatar shugaba Tinubu na ciwo bashin ₦1.77tr

-

 

Majalisar dattawa ta amince da bukatar shugaba Tinubu na ciwo bashin ₦1.77tr 

Majalisar dattijai ta Nijeriya ta amince da bukatar shugaban kasa Bola Tinubu ya ciyo bashin Naira tiriliyan 1.77, kwatankwacin naira biliyan 2.2 domin cike gibin kasafin kudin 2024.

Wannan na zuwa ne bayan bayan da aka kada kuri’ar amincewa da bukatar, a zaman majalisar wanda mataimakin shugaban majalisar Barau Jibrin ya jagoranta. 

Majalisar ta amince da wannan bashin ne bayan karɓar rahoton kwamitin kula da basukan gida da waje karkashin jagorancin Sanata Wammako Magatarkada. 

Shugaban kasar ya mika bukatar ne a ranar Talata, domin cike wani bangare na gibin kasafin kudin shekarar 2024 da ya kai naira Tiriliyan 9.7.

LEAVE A REPLY

Please enter your comment!
Please enter your name here

Sabbin Labarai

Rukunin farko na maniyyatan jihar Bauchi a Nijeriya, sun tashi zuwa Saudiyya- NAHCON

Hukumar aikin Hajji ta Nijeriya ta bayyana cewa maniyyata 2,520 ne daga cikin jihar Bauchi za su halarci aikin Hajjin bana na 2025 a kasar...

An saki ‘Yan jaridar Sahara FM da aka tsare a Agadez

Rahotanni daga Jamhuriyar Nijar na nuna cewa an saki ‘yan jarida uku na gidan rediyon Sahara FM da ke Agadez bayan da aka tsare su...

Mafi Shahara