DCL Hausa Radio
Kaitsaye

Shugaba Tinubu ya rubuta wa majalisa, yana neman ta amince da nadin Janar Oluyede a matsayin babban hafsan sojin kasa na Nijeriya

-

A cikin wasikar da ya rubuta wa shugaban majalisar Dattawa Sanata Godswill Akpabio da kakakin majalisar wakilai Hon Tajuddeen Abbas, Shugaba Tinubu ya bukaci majalisun sun tabbatar da nadin bisa la’akari da tanadin doka a sashe na 218(2) na kundin tsarin mulkin Nijeriya da aka yi wa gyara a 1999 da kuma sashe na 18(1) na dokar da ta kafa rundunar soji.
Shugaba Tinubu dai ya nada Janar Oluyede a matsayin mukaddashin babban hafsan sojin kasa na Nijeriya a ranar 30 ga watan Oktoba, 2024 bayan jinya da Janar Lagbaja ya tafi, ba a ma jima ba, Janar Lagbaja ya rasu a ranar 5 ga watan Nuwamba.
Kafin nadin nasa, Janar Oluyede shi ne kwamandan rundunar sojin kundumbala da ke Jani, jihar Kaduna.

LEAVE A REPLY

Please enter your comment!
Please enter your name here

Sabbin Labarai

Kashi 8 cikin 100 na ‘yan Nijeriya ne kawai ke iya wanke hannu yadda ya kamata a cewar UNICEF

Asusun tallafawa kananan yara na Majalisar Dinkin Duniya UNICEF ya ce kaso 92 cikin 100 na 'yan Nijeriya ba sa iya wanke hannu yadda ya...

Majalisar wakilan Nijeriya ta gayyaci Gwamnan babban bankin kasar CBN kan wasu cajin kudade da bankuna ke yi wa al’umma

Majalisar wakilan Nijeriya ta gayyaci Gwamnan babban bankin CBN, Olayemi Cardoso, tare da shugabannin manyan bankuna domin bayyana dalilin cajin kudade ba tare da daliliba...

Mafi Shahara