DCL Hausa Radio
Kaitsaye

Shugaba Tinubu ya rubuta wa majalisa, yana neman ta amince da nadin Janar Oluyede a matsayin babban hafsan sojin kasa na Nijeriya

-

A cikin wasikar da ya rubuta wa shugaban majalisar Dattawa Sanata Godswill Akpabio da kakakin majalisar wakilai Hon Tajuddeen Abbas, Shugaba Tinubu ya bukaci majalisun sun tabbatar da nadin bisa la’akari da tanadin doka a sashe na 218(2) na kundin tsarin mulkin Nijeriya da aka yi wa gyara a 1999 da kuma sashe na 18(1) na dokar da ta kafa rundunar soji.
Shugaba Tinubu dai ya nada Janar Oluyede a matsayin mukaddashin babban hafsan sojin kasa na Nijeriya a ranar 30 ga watan Oktoba, 2024 bayan jinya da Janar Lagbaja ya tafi, ba a ma jima ba, Janar Lagbaja ya rasu a ranar 5 ga watan Nuwamba.
Kafin nadin nasa, Janar Oluyede shi ne kwamandan rundunar sojin kundumbala da ke Jani, jihar Kaduna.

LEAVE A REPLY

Please enter your comment!
Please enter your name here

Sabbin Labarai

Jam’iyyar ADC ta fara rajista da tantance mambobi na kwanaki 90 a fadin Nijeriya

Jam’iyyar African Democratic Congress (ADC) ta fara shirin rajista, tantancewa da kuma jawo sabbin mambobi na tsawon kwanaki 90 a fadin Nijeriya, domin karfafa jam’iyyar...

Ya kamata a haramta amfani da kafafen sada zumunta ga ’yan kasa da shekara 16 a Nijeriya – Femi Falana

Babban lauya kuma SAN, Femi Falana, ya bukaci a haramta amfani da kafafen sada zumunta ga yara ’yan kasa da shekara 16 a Nijeriya, yana...

Mafi Shahara