DCL Hausa Radio
Kaitsaye

Tarin bashin da kake ciyowa ke jikkata tattalin arzikin Nijeriya, sakon Atiku Abubakar ga Shugaba Tinubu

-

Tsohon mataimakin shugaban kasa Atiku Abubakar kuma dan takarar shugaban kasa na jam’iyyar PDP a zaben da ya gabata, ya ce tarin bashin da gwamnatin APC ke ciyowa na kassara tattalin arzikin kasar.

Atiku ya kuma zargi majalisar dokoki ta kasar da zama taimakawa wajen jefa kasar cikin bashi.

Da yake martani kan bashin da majalisar ta amince Tinubu ya ciyo na baya-bayannan, Atiku ya ambato wani rahoto na bankin duniya wanda ya ce ya dora Nijeriya a mataki na uku cikin kasashen da tulin bashi ya yi wa yawa.

Tsohon shugaban ya bayyana damuwa aka yadda gwamnatin ke ci gaba da cin bashi, duk da cewa a watan Yuli shugaba Tinubu ya ce hukumar tattara haraji ta kasa da hukumar kwastam sun samar da kudade ga kasar wadanda ba a taba gani ba.

 

LEAVE A REPLY

Please enter your comment!
Please enter your name here

Sabbin Labarai

An saka ranar da za a fitar da sakamakon binciken zargin alaka da muggan kwayoyi da ya hada da Shugaba Tinubu na Nijeriya

An saka ranar da za a fitar da sakamakon binciken zargin alaka da muggan kwayoyi da ya hada da Shugaba Tinubu na Nijeriya. Ana dai...

Za mu iya cin zabenmu ko babu ku, kalaman Elrufa’i ga gwamnonin Nijeriya

  Tsohon Gwamnan Jihar Kaduna, Malam Nasir El-Rufai, ya bayyana cewa sabuwar kawancen jam’iyyu adawa na da karfin da zai kayar da Shugaba Bola Ahmed Tinubu...

Mafi Shahara