DCL Hausa Radio
Kaitsaye

Masu dauke da cutar HIV miliyan 1.6 ne daga cikin mutum miliyan 2 ne ke karbar magani a Nijeriya

-

Shugaban hukumar da ke yaki da cuta mai karya garkuwa jiki a Nijeriya Dr Temitope Ilori, ta ce akalla mutum miliyan 1.6 ne daga cikin mutane miliyan biyu dake fama da cuta mai karya garkuwar jiki ta HIV, ke karbar magani a Nijeriya.
Dr Temitope Ilori, ta ce wannan cutar ta fi kama wadanda ke tsakanin shekaru 15 zuwa 65, kuma karfin yaduwarta a kasar yana kashi 1.4
Ta bayyana hakan ne a wurin wani taro da aka shirya gabanin bukin ranar yaki da cutar AIDS da ya gudana a Abuja.
An ware ranar 1 ga watan Disamban kowace shekara ne domin wayar da kan al’ummar duniya akan irin hadarin wannan cutar tare da karfafawa wadanda ke rayuwa da wannan cutar mai karya garkuwar jiki.

LEAVE A REPLY

Please enter your comment!
Please enter your name here

Sabbin Labarai

El-Rufai ya nemi Ribadu ya yi karin haske kan ‘gubar’ thallium sulphate mai matukar hatsari

Tsohon gwamnan jihar Kaduna, Malam Nasir El-Rufai, ya bukaci Mai Bai wa Shugaban Kasa Shawara Kan harkokin tsaro Malam Nuhu Ribadu, da ya fayyace rahotannin...

Hadin kan siyasa na karuwa a Kano – Gwaman Kano

Gwamnan Kano State, Abba Kabir Yusuf, ya ce ana samun ci gaba a hadin kan siyasa a jihar, yana mai fatan rikicin masarautar Kano zai...

Mafi Shahara