DCL Hausa Radio
Kaitsaye

Akalla mutum 56 sun yi rasa rayukansu a mummunan turmutsitsi da ya faru a kasar Guinea.

-

 

Google search engine
Gwamnatin mulkin sojin kasar Guinea ta ce akalla mutum 56 sun mutu sakamakon wani mummunan turmutsitsi da ya faru a N’Zerekore, birni na biyu mafi girma a kasar.
Sanarwar da sojojin suka fitar ta ce turmutsitsin ya faru ne sanadiyar wani rikici tsakanin magoya bayan kwallon kafa da aka gudanar jiya Lahadi, lamarin da ya janyo hasarar rayukan mutane da dama.
Kafofin yada labarai na kasar Guinea sun ruwaito cewa an shirya wasar ne domin murnar zagayowar ranar da shugaban mulkin sojan kasar Mamadi Doumbouya ya yi juyin mulki tare da nada kan sa a matsayin shugaban kasa.

LEAVE A REPLY

Please enter your comment!
Please enter your name here

Sabbin Labarai

Idan rikicin PDP ya ki ci, ya ki cinyewa za mu shiga kawance in ji Sule Lamido

Tsohon Gwamnan Jihar Jigawa, Alhaji Sule Lamido, ya bayyana cewa dole na iya sanyawa jam’iyyar ta shiga kawance da wasu jam’iyyu idan ƙoƙarin da ake...

‘Yan sandan Nijeriya sun sanar da dawo da aiwatar da dokar lasisin gilashin mota mai duhu

Rundunar ‘Yan Sandan Nijeriya ta sanar da cewa za ta sake fara aiwatar da dokar lasisin gilashin mota mai duhu (Tinted Glass Permit), duk da...

Mafi Shahara