DCL Hausa Radio
Kaitsaye

Ba na jayayya da Shugaba Tinubu, kira kawai nake da a kara yin tuntuba kan dokar haraji – Gwamna Zulum

-

Gwamnan jihar Borno, Farfesa Babagana Umara Zulum, ya yi kira da a kara duba na tsanaki kan kudirin sake fasalin haraji da majalisar dokokin Najeriya ke nazari a kai, inda ya ce ba ya adawa da Shugaba Bola Ahmed Tinubu. 
Zulum ya bayyana haka ne ta cikin wani shirin siyasa na gidan Talabijin na Channels, inda ya jaddada muhimmancin hada hannu da masu ruwa da tsaki don magance dukkan matsalolin da ke tattare da kudirin. 
A cikin wata sanarwa da mai ba shi shawara na musamman kan harkokin yada labarai Dauda Iliya, ya fitar a Litinin din nan, Gwamna Zulum ya ce “tuntuba, babbar jigo ce ga al’ummar da ta rungumi tafarkin dimokuradiyya.”
Gwamnan ya nuna damuwarsa, tare da yin gargadin cewa wannan kuduri zai amfanar da jihohi kamar Lagos da Rivers ne kawai, abin da zai iya jefa sauran jihohin cikin mawuyacin hali.

LEAVE A REPLY

Please enter your comment!
Please enter your name here

Sabbin Labarai

Rashin tabbas da matsalolin tsaro na barazana ga burin ECOWAS na 2050 – Shugaban ECOWAS, Touray

Shugaban kungiyar ECOWAS, Omar Touray, ya ce rashin tabbas a duniya, matsalolin tsaro da matsin tattalin arziki na hana kungiyar cimma burinta na Vision 2050,...

An yi ajalin wata mace mai juna biyu da wani karamin yaro a cikin birnin Kano

Al’ummar Sheka Sabuwar Gandu a karamar hukumar Kano Municipal sun shiga firgici a daren Asabar bayan wasu da ba a san ko su waye ba...

Mafi Shahara