DCL Hausa Radio
Kaitsaye

Kotu ta yanke wa masu garkuwa da mutane hukuncin kisa a Jigawa

-

Kotu ta yanke wa masu garkuwa da mutane hukuncin kisa

Wata babbar kotu a Jihar Jigawa ta yanke wa wasu masu garkuwa da mutane hukunci  kisa ta hanyar rataya.

Da ya ke zartar da hukunci alkalin kotun mai shari’a Mohammed Musa Kaugama ya ce an sami mutanen biyu da laifuka bakwai da suka hada da yin garkuwa da mutune da hada baki da fashi da makami da haura gidan mutane.

Google search engine

A ranar 21 ga watan Yunin 2021 ne mutanen biyu wato Sani Mohammed da Babannan Saleh, dauke da makami suka haura gidan Hamidi Abdu da ke garin Shangel a karamar Hukumar Ringim inda suka kwace masa kudade masu yawa sannan suka ta fi da shi, daga baya suka nemi kudin fansa har naira miliyan 12 kafin su sake shi.

LEAVE A REPLY

Please enter your comment!
Please enter your name here

Sabbin Labarai

Goyon bayan Atiku ga Obi zai kawo karshen mulkin Tinubu a 2027 – Jam’iyyar Labour

Jam'iyyar Labour party ta bayyana cewa ta hanyar hada kai ne kawai za a iya kawo karshen mulkin shugaban Nijeriya Bola Tinubu a 2027. Tsagin jam'iyyar...

Tinubu ya gargadi Alkalan Nijeriya da kada su karkata ga cin hanci ko rashin adalci

Shugaban ƙasa Bola Ahmed Tinubu ya yi kira ga alkalai da sauran ma’aikatan shari’a a Najeriya da su ci gaba da zama masu gaskiya, adalci,...

Mafi Shahara