DCL Hausa Radio
Kaitsaye

Babu rashin jituwa tsakanin mu da gwamnoni kan cin gashin kan kananan hukumomi –Shugaba Tinubu

-

 

Shugaba Tinubu

Google search engine

Shugaban Nijeriya Bola Ahmad Tinubu ya yi kira da gwamnatocin jihohi da su hada gwiwa domin tunkarar kalubalen da ke addabar kananan hukumomi a kasar.

Shugaba Tinubu ya yi wannan kiran ne a yayin bikin sabuwar shekara tare da mataimakin shugaban kasa Kashim Shettima da wasu gwamnonin Nijeriya da suka yi a gidansa da ke Legas ranar Laraba.

Da yake bayyana kudirinsa na ci gaban kananan hukumomi, a cikin wata sanarwa da mai taimaka wa shugaban kasar kan harkokin yada labarai, Bayo Onanuga ya fitar, ya jaddada muhimmancin ‘yan cin gashin kai ga kananan hukumomi wajen ci gaban kasa da tare da kawar da rade radin rashin jituwa tsakanin sa da gwamnonin.

Inda ya ce babu wata matsala a tsakanin su,illa kokarin kawo sauyi mai dorewa ga kasa ta hanyar baiwa kananan hukumomi dama.

LEAVE A REPLY

Please enter your comment!
Please enter your name here

Sabbin Labarai

SERAP ta maka Akpabio da Abbas kotu kan zargin cin hanci na Naira miliyan 3 a majalisar dokoki

Kungiyar SERAP ta shigar da shugaban majalisar dattawa, Sanata Godswill Akpabio, da kakakin majalisar wakilai, Tajudeen Abbas, kotu saboda kin bincikar zargin cewa ‘yan majalisa...

Taimako Nijeriya ke buƙata daga Amurka wajen yaki da matsalar tsaro ba tsoratar da ita ba – Sanata Rabi’u Musa Kwankwaso

Tsohon gwamnan Jihar Kano, kuma Madugun Kwankwasiyya, Sanata Rabiu Musa Kwankwaso, ya bayyana damuwarsa kan yadda Shugaban Amurka Donald Trump ke ta yin maganganu masu...

Mafi Shahara