DCL Hausa Radio
Kaitsaye

Babu rashin jituwa tsakanin mu da gwamnoni kan cin gashin kan kananan hukumomi –Shugaba Tinubu

-

 

Shugaba Tinubu

Google search engine

Shugaban Nijeriya Bola Ahmad Tinubu ya yi kira da gwamnatocin jihohi da su hada gwiwa domin tunkarar kalubalen da ke addabar kananan hukumomi a kasar.

Shugaba Tinubu ya yi wannan kiran ne a yayin bikin sabuwar shekara tare da mataimakin shugaban kasa Kashim Shettima da wasu gwamnonin Nijeriya da suka yi a gidansa da ke Legas ranar Laraba.

Da yake bayyana kudirinsa na ci gaban kananan hukumomi, a cikin wata sanarwa da mai taimaka wa shugaban kasar kan harkokin yada labarai, Bayo Onanuga ya fitar, ya jaddada muhimmancin ‘yan cin gashin kai ga kananan hukumomi wajen ci gaban kasa da tare da kawar da rade radin rashin jituwa tsakanin sa da gwamnonin.

Inda ya ce babu wata matsala a tsakanin su,illa kokarin kawo sauyi mai dorewa ga kasa ta hanyar baiwa kananan hukumomi dama.

LEAVE A REPLY

Please enter your comment!
Please enter your name here

Sabbin Labarai

Babu adawa a jihar Plateau a zaben 2027 – Caleb Muftwang

Gwamnan Jihar Plateau, Caleb Manasseh Mutfwang, ya bayyana cewa zuwa zaben 2027 jam’iyyarsa ba za ta samu adawa a jihar ba. Ya fadi hakan ne...

Obasanjo ya musanta rubuta sanarwar mutuwarsa

Tsohon Shugaban Nijeriya, Olusegun Obasanjo, ya musanta wani rubutu da ke yawo a kafafen sada zumunta da ke ikirarin cewa ya fitar da sanarwar mutuwarsa. Rubutun...

Mafi Shahara