HomeUncategorizedBabban hafsan sojin Lebanon ya zama sabon shugaban kasar

Babban hafsan sojin Lebanon ya zama sabon shugaban kasar

-

 

Joseph Aoun

An kada kuri’ar zaben shugaban kasar Lebanon inda aka zabi Joseph Aoun a matsayin shugaban kasa a zagaye na biyu na zaben da ‘yan majalisar dokokin kasar a ranar Alhamis, wanda ya kawo karshen rashin shugaba da kasar ke fama da shi , tare da shafe shekaru biyu ana kasar na fama da rikici.

Kamfanin dillancin labarai na AFP ya rawaito cewa Kakakin majalisar kasar Nabih Berri ne ya sanar da cewa Joseph Aoun ne shugaban kasa, bayan ya samu kuri’u 99 daga cikin 128 bayan da aka gaza samun kuri’u da ake bukata a zagayen farko da aka gudanar.

Tuni dai aka rantsar da sabon shugaban mai shekaru 61, wanda ake kyautata zaton zai samu goyon bayan Amurka, Saudi Arabia da kasashen yammacin duniya.

LEAVE A REPLY

Please enter your comment!
Please enter your name here

LATEST POSTS

Sarkin Daura ya nada Hamza Sule Sarautar Sadaukin Kasar Hausa

Maimartaba Sarkin Daura Alh Faruk Umar Faruk ya nada Hon. Hamza Sulaiman Faskari Kwamishinan mahallin jihar katsina sarautar Sadaukin Kasar Hausa a fadarsa dake garin...

Kawance domin kayar da Tinubu a 2027 ba zai yi wani tasiri ba, bata lokaci ne kawai, in ji dan jam’iyyar PDP Ayo Fayose

Tsohon gwamnan jihar Ekiti, Ayo Fayose, ya yi watsi da gamayyar jam’iyyun adawa na siyasa da ake tattaunawa a kai, da nufin kifar da Gwamnatin...

Babu wanda ya hana Kasshim Shettima shiga fadar Shugaban kasa ta Villa, labarin ba ya da tushe bare makama – Mai magana da yawunsa...

Babban Mataimaki na Musamman ga Shugaban Kasa kan Harkokin Yada Labarai Stanley Nkwocha,ya bayyana labarin da ke yawo a kafafan sada zumunta, dangane da hana...

Jiga-jigan APC sun tattaru a Abuja, sun tabbatar wa da Shugaba Tinubu zai yi nasara da gagarumin rinjaye a zaben 2027

Jiga-jigan jam’iyyar APC mai mulki sun gudanar da wani gangami a Abuja, inda suka bayyana cewa shugaba Bola Ahmed Tinubu zai samu gagarumin rinjaye a...

Most Popular

spot_img