DCL Hausa Radio
Kaitsaye

Shugaba Tinubu ya amince da haramta luwadi a rundunar sojin Nijeriya

-

Shugaba Tinubu

An haramta wa jami’an sojin Nijeriya yin luwadi, madigo, sanya kayayyakin da basu dace ba, da sauran abubuwan  da ake ganin sun saba wa ka’idojin rundunar.

Google search engine

Haka zalika an hana jami’an huda jiki da nufin  saka Sarka ko Dan kunne ko kuma zanen hotuna a jikin fata wato  (Tatoo )a jiki, da shan  Barasa a yayin da suke aiki ko basa aiki.

Wannan umurnin yana kunshe ne acikin sashe na 26 na kundun rundunar da aka yi wa kwaskwarima da shugaba Bola Tinubu ya sanya wa hannu a ranar 16 ga Disamba, 2024.

A wata takarda da jaridar Punch ta samu a ranar Asabar wani bangaren ta yana cewa, “Bai kamata jami’in soji su dinga aikata  luwadi, madigo, da sauran munanan ayyuka ba.

 Haka zalika ba a amince wani jami’in rundunar soji ya dunga irin wayannan ayyuka ba ciki harda yin “Tattoo” dama shan abubuwan da zasu kautarwa mutum hankali a loka2cin yana kan aiki ko baya aiki.

LEAVE A REPLY

Please enter your comment!
Please enter your name here

Sabbin Labarai

Gwamna Zulum zai ba duk dan Borno da ke hijira a Kamaru N500,000

Gwamnan Jihar Borno, Farfesa Babagana Umara Zulum, ya bayyana cewa gwamnatin jiharsa za ta ba kowane ɗan gudun hijira ɗan Borno da yake a Kamaru...

Najeriya da Saudiyya sun rattaba hannu kan yarjejeniyar tsaro

Najeriya da Masarautar Saudiyya sun kulla sabuwar yarjejeniya ta shekaru biyar domin ƙarfafa haɗin gwiwar tsaro da dangantakar soja tsakanin kasashen biyu. A cewar wata sanarwa...

Mafi Shahara