DCL Hausa Radio
Kaitsaye

Kotu ta amince da gyara kan tuhume-tuhumen da ake yi wa tsohon Ministan wutar lantarki Dakta Olu Agunloye.

-

 

Google search engine

Babbar kotun birnin tarayya Abuja, ta amince da bukatar hukumar yaki da masu yi wa tattalin arzikin kasa zagon kasa na yin kwaskwarima kan tuhumar da ake yi wa tsohon ministan wutar lantarki, Dakta Olu Agunloye.

Mai shari’a Jude Onwuegbuzie ya amince da gyaran ne yayin da yake yanke hukunci kan rashin amincewar wanda ake kara kan karar da aka shigar a ranar 25 ga watan Yuni, 2024.

Dakta Olu Agunloye dai na fuskantar tuhumar laifuka bakwai da EFCC ta shigar a gaban kotu mai lamba FCT/HC/CR/617/2023.

Laifukan sun shafi na  jabu, kin bin umarnin shugaban kasa, da kuma aikata  almundahana da suka shafi aikin tashar wutar lantarki ta Mambila a jihar Taraba.

LEAVE A REPLY

Please enter your comment!
Please enter your name here

Sabbin Labarai

INEC na duba buƙatun kungiyoyi 110 da ke neman rigista a matsayin jam’iyyun siyasa a Najeriya

Hukumar zabe ta kasa INEC ta bayyana cewa ta karɓi wasikun buƙatun rajistar sabbin jam’iyyu 110 daga kungiyoyi daban-daban har zuwa Litinin, 23 ga watan...

PDP ta maido wa Samuel Anyanwu mukaminsa na sakataren jam’iyyar na kasa

PDP ta maido wa Samuel Anyanwu mukaminsa na sakataren jam'iyyar na kasa Jam’iyyar PDP ta dawo da Samuel Anyanwu a matsayin sakataren jam’iyya na kasa bayan...

Mafi Shahara