DCL Hausa Radio
Kaitsaye

Kotu ta amince da gyara kan tuhume-tuhumen da ake yi wa tsohon Ministan wutar lantarki Dakta Olu Agunloye.

-

 

Google search engine

Babbar kotun birnin tarayya Abuja, ta amince da bukatar hukumar yaki da masu yi wa tattalin arzikin kasa zagon kasa na yin kwaskwarima kan tuhumar da ake yi wa tsohon ministan wutar lantarki, Dakta Olu Agunloye.

Mai shari’a Jude Onwuegbuzie ya amince da gyaran ne yayin da yake yanke hukunci kan rashin amincewar wanda ake kara kan karar da aka shigar a ranar 25 ga watan Yuni, 2024.

Dakta Olu Agunloye dai na fuskantar tuhumar laifuka bakwai da EFCC ta shigar a gaban kotu mai lamba FCT/HC/CR/617/2023.

Laifukan sun shafi na  jabu, kin bin umarnin shugaban kasa, da kuma aikata  almundahana da suka shafi aikin tashar wutar lantarki ta Mambila a jihar Taraba.

LEAVE A REPLY

Please enter your comment!
Please enter your name here

Sabbin Labarai

Limaman coci sun musanta zargin kisan Kiristoci a Nijeriya

Wasu limaman coci sun yi watsi da zargin Amurka da ke cewa ana gudanar da kisan kiyashi kan Kiristoci a Nijeriya.   Limaman sun mayar da martani...

Mun kashe Naira 100bn a fannin tsaron Borno cikin 2025 – Gwamna Zulum

Gwamnan jihar Borno Babagana Umara Zulum ya nuna damuwa da yadda ake kashe makuden kudade a fannin tsaro, yana mai cewa gwamnatinsa ta kashe Naira...

Mafi Shahara