DCL Hausa Radio
Kaitsaye

Kotu ta amince da gyara kan tuhume-tuhumen da ake yi wa tsohon Ministan wutar lantarki Dakta Olu Agunloye.

-

 

Google search engine

Babbar kotun birnin tarayya Abuja, ta amince da bukatar hukumar yaki da masu yi wa tattalin arzikin kasa zagon kasa na yin kwaskwarima kan tuhumar da ake yi wa tsohon ministan wutar lantarki, Dakta Olu Agunloye.

Mai shari’a Jude Onwuegbuzie ya amince da gyaran ne yayin da yake yanke hukunci kan rashin amincewar wanda ake kara kan karar da aka shigar a ranar 25 ga watan Yuni, 2024.

Dakta Olu Agunloye dai na fuskantar tuhumar laifuka bakwai da EFCC ta shigar a gaban kotu mai lamba FCT/HC/CR/617/2023.

Laifukan sun shafi na  jabu, kin bin umarnin shugaban kasa, da kuma aikata  almundahana da suka shafi aikin tashar wutar lantarki ta Mambila a jihar Taraba.

LEAVE A REPLY

Please enter your comment!
Please enter your name here

Sabbin Labarai

Buhari mutum ne mai girmama al’adu da masarautu – Sarkin Musulmi

Sarkin Musulmi, Alhaji Muhammad Sa’ad Abubakar, ya shiga sahun wadanda ke jimamin rasuwar tsohon Shugaban Najeriya, Muhammadu Buhari, wanda ya rasu a wani asibiti a...

An rufe ofishin jakadancin Amurka na Abuja da Legas don jimamin rasuwat Buhari

Ofishin jakadancin Amurka da ke Abuja da kuma na Legas za su kasance a rufe a ranar Talata, 15 ga Yuli, 2025, domin girmamawa da...

Mafi Shahara