DCL Hausa Radio
Kaitsaye

Hukumar shari’a a Kano ta yi wa wani ma’aikacin ta ritayar dole bisa zargin karbar cin hanci

-

Google search engine

Hukumar da ke kula da harkokin shari’a ta jihar Kano (JSC), ta dakatar da wani jami’in ta tare da yi wa wani ritayar dole saboda karbar cin hanci.

Kakakin hukumar, Baba Jibo, shi ya fitar da wata sanarwa inda ya bayyana cewa hukumar ta amice da hukuncin da aka dauka kan ma’aikatan a taronta na 79 da ta gudanar a ranar 6 ga watan Fabrairu wanda babban alkalin jihar, Dije Aboki ta jagoranta.

Ya ce binciken da kwamitin sauraron korafe-korafen jama’a na sashen shari’a (JPCC) ya yi dangane da karar da wani Alhaji Sani Bozo Rimin Gado ya shigar a kan Hudu Idris wato magatakarda a kotun shari’a ta Upper Shari’a Gwarzo da Abba Bala Gwarzo, mai gadi a kotun.

Ana zargin  jami’an kotunan biyu da yi musu barazana da kuma neman kudi ba bisa ka’ida ba. 

Bayan wani kwakkwaran bincike, mutanen biyu sun bayyana a gaban hukumar ta JPCC, inda suka amsa laifin cewa suna da hannu a cikin almundahana da ya kai na N214,000.

LEAVE A REPLY

Please enter your comment!
Please enter your name here

Sabbin Labarai

ECOWAS ta amince John Mahama ya mata takarar shugabancin AU a 2027

Majalisar Ministocin ECOWAS ta amince da Shugaban Ghana, John Mahama, a matsayin ɗan takarar kungiyar da zai nemi kujerar Shugaban Kungiyar Tarayyar Afrika (AU) a...

Neman tazarce na hana wasu gwamnoni yin aiki – Umar Bago

Neman tazarce a 2027, ne ke hana ni korar jami'an da ba su da amfani a gwamnatina - In ji Gwamna Umar Bago Gwamnan jihar Neja,...

Mafi Shahara