DCL Hausa Radio
Kaitsaye

Hukumar shari’a a Kano ta yi wa wani ma’aikacin ta ritayar dole bisa zargin karbar cin hanci

-

Google search engine

Hukumar da ke kula da harkokin shari’a ta jihar Kano (JSC), ta dakatar da wani jami’in ta tare da yi wa wani ritayar dole saboda karbar cin hanci.

Kakakin hukumar, Baba Jibo, shi ya fitar da wata sanarwa inda ya bayyana cewa hukumar ta amice da hukuncin da aka dauka kan ma’aikatan a taronta na 79 da ta gudanar a ranar 6 ga watan Fabrairu wanda babban alkalin jihar, Dije Aboki ta jagoranta.

Ya ce binciken da kwamitin sauraron korafe-korafen jama’a na sashen shari’a (JPCC) ya yi dangane da karar da wani Alhaji Sani Bozo Rimin Gado ya shigar a kan Hudu Idris wato magatakarda a kotun shari’a ta Upper Shari’a Gwarzo da Abba Bala Gwarzo, mai gadi a kotun.

Ana zargin  jami’an kotunan biyu da yi musu barazana da kuma neman kudi ba bisa ka’ida ba. 

Bayan wani kwakkwaran bincike, mutanen biyu sun bayyana a gaban hukumar ta JPCC, inda suka amsa laifin cewa suna da hannu a cikin almundahana da ya kai na N214,000.

LEAVE A REPLY

Please enter your comment!
Please enter your name here

Sabbin Labarai

Gwamnatin Tinubu ta fitar da Naira biliyan 2.3 don biyan bashin albashi da karin girma na malaman jami’o’i

Gwamnatin Tarayya ta bayyana cewa ta saki kudin da ya kai Naira biliyan 2.3 domin biyan bashin albashi da karin girma na malamai a jami’o’in...

Majalisar wakilan Nijeriya ta amince wa Tinubu ya ciyo bashin dala biliyan 2.35

Majalisar wakilai ta Nijeriya ta amince da bukatar shugaban Tinubu na neman bashin dala biliyan 2.347 daga ƙasashen waje domin cike gibin kasafin kuɗin 2025...

Mafi Shahara