DCL Hausa Radio
Kaitsaye

Kotu a Abuja ta dakatar da Majalisar Dattawa daga ladabtar da Sanata Natasha

-

 

Sanata Natasha Akpoti

Wata babbar kotun tarayya da ke Abuja ta dakatar da kwamitin da’a na majalisar dattawa da karbar koken jama’a daga ladabtar da sanata mai wakiltar Kogi ta Tsakiya, Natasha Akpoti-Uduaghan.

Alkalin kotun, Obiora Egwuatu, ya ba da umarnin ne a ranar Talata bayan wata takardar karar da lauyan Akpoti-Uduaghan ya shigar a gaban kotun.

A ranar 20 ga watan Fabrairun shekarar 2025, sanatar mai wakiltar Kogi ta tsakiya ta yi musayar kalamai da shugaban majalisar dattawa, Godswill Akpabio, kan batun sauyin wurin zama da aka yi mata.

Kin bin umarnin shugaban majalisar Godswill Akpabio da ta yi, ya janyo cece kuce a cikin majalisar da ma wajen majalisar.

LEAVE A REPLY

Please enter your comment!
Please enter your name here

Sabbin Labarai

Kwamishinan Jigawa ya mayar da rarar Naira miliyan 301 daga kudaden da aka ware don shirin ciyar da al’umma a watan Ramadan

Kwamishinan ayyuka na musamman na jihar Jigawa, Alhaji Auwalu Danladi Sankara, ya mayar da Naira miliyan 301 zuwa baitul malin jihar, daga cikin Naira biliyan...

Gwamnatin mulkin sojin Nijar ta karɓi wasikun kulla kawance daga sabbin jakadun ƙasashe 8

A ranar Juma’a, 9 ga Mayu, 2025, fadar gwamatin ta Jamhuriyar Nijar ta karɓi sabbin jakadun daga jakadun ƙasashen duniya guda takwas. Inda shugaban mulkin sojin...

Mafi Shahara