DCL Hausa Radio
Kaitsaye

Kotu a Abuja ta dakatar da Majalisar Dattawa daga ladabtar da Sanata Natasha

-

 

Sanata Natasha Akpoti

Wata babbar kotun tarayya da ke Abuja ta dakatar da kwamitin da’a na majalisar dattawa da karbar koken jama’a daga ladabtar da sanata mai wakiltar Kogi ta Tsakiya, Natasha Akpoti-Uduaghan.

Google search engine

Alkalin kotun, Obiora Egwuatu, ya ba da umarnin ne a ranar Talata bayan wata takardar karar da lauyan Akpoti-Uduaghan ya shigar a gaban kotun.

A ranar 20 ga watan Fabrairun shekarar 2025, sanatar mai wakiltar Kogi ta tsakiya ta yi musayar kalamai da shugaban majalisar dattawa, Godswill Akpabio, kan batun sauyin wurin zama da aka yi mata.

Kin bin umarnin shugaban majalisar Godswill Akpabio da ta yi, ya janyo cece kuce a cikin majalisar da ma wajen majalisar.

LEAVE A REPLY

Please enter your comment!
Please enter your name here

Sabbin Labarai

Limaman coci sun musanta zargin kisan Kiristoci a Nijeriya

Wasu limaman coci sun yi watsi da zargin Amurka da ke cewa ana gudanar da kisan kiyashi kan Kiristoci a Nijeriya.   Limaman sun mayar da martani...

Mun kashe Naira 100bn a fannin tsaron Borno cikin 2025 – Gwamna Zulum

Gwamnan jihar Borno Babagana Umara Zulum ya nuna damuwa da yadda ake kashe makuden kudade a fannin tsaro, yana mai cewa gwamnatinsa ta kashe Naira...

Mafi Shahara