DCL Hausa Radio
Kaitsaye

Kotu a Abuja ta dakatar da Majalisar Dattawa daga ladabtar da Sanata Natasha

-

 

Sanata Natasha Akpoti

Wata babbar kotun tarayya da ke Abuja ta dakatar da kwamitin da’a na majalisar dattawa da karbar koken jama’a daga ladabtar da sanata mai wakiltar Kogi ta Tsakiya, Natasha Akpoti-Uduaghan.

Google search engine

Alkalin kotun, Obiora Egwuatu, ya ba da umarnin ne a ranar Talata bayan wata takardar karar da lauyan Akpoti-Uduaghan ya shigar a gaban kotun.

A ranar 20 ga watan Fabrairun shekarar 2025, sanatar mai wakiltar Kogi ta tsakiya ta yi musayar kalamai da shugaban majalisar dattawa, Godswill Akpabio, kan batun sauyin wurin zama da aka yi mata.

Kin bin umarnin shugaban majalisar Godswill Akpabio da ta yi, ya janyo cece kuce a cikin majalisar da ma wajen majalisar.

LEAVE A REPLY

Please enter your comment!
Please enter your name here

Sabbin Labarai

Gasar cin kofin kasashen nahiyar Afirka AFCON za ta koma duk bayan shekaru 4 – CAF

Hukumar kwallon kafa ta nahiyar Afrika CAF, ta sanar da cewa gasar cin kofin kasashen Afrika AFCON, za ta koma duk bayan shekara huɗu bayan...

Tinubu ya ziyarci jihar Borno domin bude ayyuka

Shugaba Tinubu, ya ziyarci Maiduguri, babban birnin Jihar Borno, domin ƙaddamar da manyan ayyuka da halartar bikin auren ɗan tsohon gwamnan jihar, Sanata Ali Modu...

Mafi Shahara