DCL Hausa Radio
Kaitsaye

Gwamnatin jihar Kebbi ta nemi gwamnatin tarayya da ta kafa sansanin soji a karamar hukumar Arewa

-

Nasir Idris

Gwamnan jihar Kebbi Nasir Idris, ya roki a kafa sansanin soji a karamar hukumar Arewa da ke jihar domin inganta tsaro a yankin.

Nasir Idris ya yi wannan roko ne a wata hira da manema labarai jim kadan bayan ziyarar jaje da ya kai sansanin ‘yan gudun hijira da ke Kangiwa, hedikwatar karamar hukumar Arewa a ranar Laraba.

Google search engine

Kamfanin dillancin labaran Nijeriya, NAN ya rawaito cewa a ranar Lahadi 9 ga watan Maris, wasu da ake zargin ‘yan ta’addar Lakurawa ne sun kai hari tare da halaka mutane 11 tare da kona kauyuka bakwai a karamar hukumar ta Arewa.

Kauyukan sun hada da, Dogon Daji, Danmarke, Yar Goru, Tambo, Birnin Debi, Garin Nagoro da Garin Rugga, duk a karamar hukumar Arewa.

Gwamnan ya bayyana bakin cikinsa kan wannan mummunan lamarin da ya janyo hasarar rayuka tare da yin kira ga gwamnatin tarayya da ta duba yiwuwar kafa sansanin soji a karamar hukumar.
 

LEAVE A REPLY

Please enter your comment!
Please enter your name here

Sabbin Labarai

Buhari mutum ne mai girmama al’adu da masarautu – Sarkin Musulmi

Sarkin Musulmi, Alhaji Muhammad Sa’ad Abubakar, ya shiga sahun wadanda ke jimamin rasuwar tsohon Shugaban Najeriya, Muhammadu Buhari, wanda ya rasu a wani asibiti a...

An rufe ofishin jakadancin Amurka na Abuja da Legas don jimamin rasuwat Buhari

Ofishin jakadancin Amurka da ke Abuja da kuma na Legas za su kasance a rufe a ranar Talata, 15 ga Yuli, 2025, domin girmamawa da...

Mafi Shahara