DCL Hausa Radio
Kaitsaye

Gwamnatin jihar Kebbi ta nemi gwamnatin tarayya da ta kafa sansanin soji a karamar hukumar Arewa

-

Nasir Idris

Gwamnan jihar Kebbi Nasir Idris, ya roki a kafa sansanin soji a karamar hukumar Arewa da ke jihar domin inganta tsaro a yankin.

Nasir Idris ya yi wannan roko ne a wata hira da manema labarai jim kadan bayan ziyarar jaje da ya kai sansanin ‘yan gudun hijira da ke Kangiwa, hedikwatar karamar hukumar Arewa a ranar Laraba.

Kamfanin dillancin labaran Nijeriya, NAN ya rawaito cewa a ranar Lahadi 9 ga watan Maris, wasu da ake zargin ‘yan ta’addar Lakurawa ne sun kai hari tare da halaka mutane 11 tare da kona kauyuka bakwai a karamar hukumar ta Arewa.

Kauyukan sun hada da, Dogon Daji, Danmarke, Yar Goru, Tambo, Birnin Debi, Garin Nagoro da Garin Rugga, duk a karamar hukumar Arewa.

Gwamnan ya bayyana bakin cikinsa kan wannan mummunan lamarin da ya janyo hasarar rayuka tare da yin kira ga gwamnatin tarayya da ta duba yiwuwar kafa sansanin soji a karamar hukumar.
 

LEAVE A REPLY

Please enter your comment!
Please enter your name here

Sabbin Labarai

Gwamna Abba K. Yusuf ya amince a biya tsofaffin Kansilolin gwamnatin Ganduje sama da 3000 kudin ritayarsu

Gwamna Abba K. Yusuf ya amince a biya kudin fanshon fiye da Naira biliyan 15 ga tsofaffin Kansilolin gwamnatin Ganduje sama da 3000 Wadanda abin ya...

PDP za ta tattauna da gwamnoninta kan sauya shekar da ‘ya’yanta ke yi

PDP za ta tattauna da gwamnoninta kan sauya shekar da 'ya'yanta ke yi nan da makon gobe Kwamitin gudanarwa na kasa (NWC) na jam’iyyar PDP tare da kungiyar gwamnonin...

Mafi Shahara