DCL Hausa Radio
Kaitsaye

Babu mai iya jan mu wata jam’iyya muna PDP – Sule Lamido

-

Sule Lamido

Tsohon gwamnan jihar Jigawa kuma jigo a jam’iyyar PDP, Sule Lamido, yayi watsi da kiran da tsohon gwamnan jihar Kaduna, Nasir El-Rufai ya yi na neman shugabannin jam’iyyar adawa su koma jam’iyyar SDP.

Google search engine

El-Rufai, wanda a kwanakin baya ya bayyana ficewarsa daga jam’iyyar APC zuwa SDP, ya yi wannan kiran ne a wata hira da BBC Hausa.

Wanda a yayin hirar bai ambaci sunan Sule Lamido ba, ya gayyaci manyan ‘yan adawa da suka hada da Atiku Abubakar, da Peter Obi, da Rotimi Amaechi, da Rauf Aregbesola, domin su dawo jam’iyyar SDP.

Da yake mayar da martani a wata hira ta da BBC Hausa ta yi a ranar Lahadi, Lamido ya yi watsi da gayyatar da aka yi masa a matsayin cin fuska, inda ya ce jam’iyyar PDP ce ta taimaka wajen kafa harsashin siyasar El-Rufai.

Ya kuma bayyana cewa jam’iyyar PDP ita ce ta haifi tsohon gwamnan Kaduna El-Rufai,kuma ba za su bar PDP ba.

LEAVE A REPLY

Please enter your comment!
Please enter your name here

Sabbin Labarai

Za mu fara hukunta duk wani dan kasar waje da wa’adin bizarsa ya kare a Nijeriya kuma ya ci gaba da zama – Gwamnatin...

Gwamnatin Nijeriya ta bayyana cewa yanzu tana da cikakken tsarin gano tare da cafke baƙin ƙasashen waje da suka wuce wa’adin zaman da aka ba...

Obasanjo ya nuna jarumtaka da sadaukarwa wajen yi wa Nijeriya hidima – Shugaba Tinubu

Shugaban Nijeriya Bola Ahmed Tinubu, ya taya tsohon shugaban ƙasar Olusegun Obasanjo murnar cika shekaru 89 da haihuwa. A cikin wata sanarwa da mai magana da...

Mafi Shahara