DCL Hausa Radio
Kaitsaye

Babu mai iya jan mu wata jam’iyya muna PDP – Sule Lamido

-

Sule Lamido

Tsohon gwamnan jihar Jigawa kuma jigo a jam’iyyar PDP, Sule Lamido, yayi watsi da kiran da tsohon gwamnan jihar Kaduna, Nasir El-Rufai ya yi na neman shugabannin jam’iyyar adawa su koma jam’iyyar SDP.

Google search engine

El-Rufai, wanda a kwanakin baya ya bayyana ficewarsa daga jam’iyyar APC zuwa SDP, ya yi wannan kiran ne a wata hira da BBC Hausa.

Wanda a yayin hirar bai ambaci sunan Sule Lamido ba, ya gayyaci manyan ‘yan adawa da suka hada da Atiku Abubakar, da Peter Obi, da Rotimi Amaechi, da Rauf Aregbesola, domin su dawo jam’iyyar SDP.

Da yake mayar da martani a wata hira ta da BBC Hausa ta yi a ranar Lahadi, Lamido ya yi watsi da gayyatar da aka yi masa a matsayin cin fuska, inda ya ce jam’iyyar PDP ce ta taimaka wajen kafa harsashin siyasar El-Rufai.

Ya kuma bayyana cewa jam’iyyar PDP ita ce ta haifi tsohon gwamnan Kaduna El-Rufai,kuma ba za su bar PDP ba.

LEAVE A REPLY

Please enter your comment!
Please enter your name here

Sabbin Labarai

Tsohon Minista Tanimu Turaki ya zama ɗan takarar shugabancin jam’iyyar PDP na Arewa

Jagororin jam’iyyar PDP na yankin Arewacin Nijeriya sun amince da tsohon Ministan Harkoki. A Musamman, Tanimu Turaki (SAN), a matsayin ɗan takarar da suka amince...

Jam’iyyar ADC a Kaduna ta kori mataimakin shugabanta da wasu ‘ya’yanta 8

Jam'iyyar hadaka ta ADC mai hamayya a Nijeriya reshen Kaduna ta kori mataimakin shugabanta na jihar tare da wasu manyan jami'anta guda takwas, bayan samun...

Mafi Shahara