DCL Hausa Radio
Kaitsaye

Jami’an tsaro sun dakile harin ‘yan bindiga a Katsina, tare da ajalin mutum daya

-

‘Yan sanda

Jami’an tsaro sun dakile wani hari da wasu da ake zargin ‘yan bindiga ne suka kai a karamar hukumar Danmusa da ke jihar Katsina.

Google search engine

Mai magana da yawun rundunar ‘yan sandan jihar Katsina, DSP Abubakar Sadiq, ne ya bayyana hakan a wata sanarwa da ya fitar ranar Lahadi.

Ya ce aikin da aka yi a ranar Asabar din da ta gabata ya kasance tare da hadin gwiwar ma’aikatar ayyuka ta jihar, da kuma ‘yan kungiyar sa kai ta jihar Katsina.

 A cewarsa, ‘yan bindigar sun yi yunkurin kai hari kauyen Dan Takuri na karamar hukumar Danmusa da ke jihar.

 A ranar 15 ga Maris, 2025, bayanan sirri da aka samu daga jami’an tsaro na farin kaya a Danmusa, ‘yan bindigar masu tarin yawa sun hau tsaunin Maijele da ke karamar hukumar Danmusa a yunkurin kai hari kauyen Dan Takuri.

Bayan samun labarin, ba tare da bata lokaci ba, tawagar hadin guiwar jami’an ‘yan sanda da ‘yan karkashin jagorancin DPO Danmusa suka afkawa tsaunin da ake zargin ‘yan fashin ne suke taruwa.

LEAVE A REPLY

Please enter your comment!
Please enter your name here

Sabbin Labarai

Sabon shugaban hukumar zaben ya yi alwashin dawo da ingantacce da sahihin zabe a Nijeriya

Sabon shugaban hukumar zaɓen Nijeriya, INEC, Farfesa Joash Amupitan, SAN, ya sha alwashin dawo da sahihanci da amincewar jama’a ga tsarin zaɓe na ƙasar, yana...

Ba ni ke tsoma baki a gwamnatin Kano ko raba kwangiloli ba – Rabi’u Musa Kwankwaso

Jagoran jam’iyyar NNPP kuma tsohon gwamnan Jihar Kano, Sanata Rabi’u Musa Kwankwaso, ya karyata zargin da ake yi masa na tsoma baki a harkokin mulkin...

Mafi Shahara