DCL Hausa Radio
Kaitsaye

Kungiyar SERAP ta maka Akpabio a kotu kan dakatar da Natasha Akpoti Uduaghan

-

Godswill Akpabio

Kungiyar SERAP mai fafutikar yaki da cin hanci da rashawa a Nijeriya ta yi karar shugaban Majalisar Dattawa, Godswill Akpabio, kan kin sauya matakin dakatarwar da aka yi wa Sanata Natasha Akpoti ba bisa ka’ida ba,wanda ta ce hakan take ‘yancinta ne na fadin albarkacin bakinta.

Google search engine

A kwanakin baya ne majalisar dattawa ta dakatar da Natasha Akpoti-Uduaghan na tsawon watanni shida, bayan da aka ce ta ‘yi magana ba tare da izini ba’ kuma ta ‘ki amincewa da sabuwar kujerar da aka ware mata a zauren majalisar.

A cikin karar mai lamba FHC/ABJ/CS/498/2025 da aka shigar a ranar Juma’ar da ta gabata a babbar kotun tarayya da ke Abuja, SERAP na neman da a tilasta soke dakatarwar da aka yi wa Natasha Akpoti-Uduaghan ba bisa ka’ida ba, a maido da ita, tare da dawo mata da dukkan hakkokinta.

SERAP na neman Majalisar Dattawa da ta dakatar da daukar duk wani matakin ladabtarwa a kan Natasha Akpoti-Uduaghan.

LEAVE A REPLY

Please enter your comment!
Please enter your name here

Sabbin Labarai

kungiya a cikin APC ta gargadi shugaban jam’iyyar game da hana gwamnan Filato shiga jam’iyyar APC

Wata ƙungiya mai goyon bayan shugaban ƙasa Bola Tinubu a jam’iyyar APC, mai suna Renewed Hope Advocates for Tinubu 2027, ta gargadi shugaban jam’iyyar na...

Gwamnatin Kamaru ta takaita amfani da intanet yayin da ake zaman dar-dar game da sakamakon zaben shugaban kasa

Gwamnatin ƙasar Kamaru ta takaita amfani da intanet a wasu sassa na ƙasar a ranar Alhamis, yayin da ake zaman dar-dar saboda jinkirin bayyana sakamakon...

Mafi Shahara