DCL Hausa Radio
Kaitsaye

Kungiyar SERAP ta maka Akpabio a kotu kan dakatar da Natasha Akpoti Uduaghan

-

Godswill Akpabio

Kungiyar SERAP mai fafutikar yaki da cin hanci da rashawa a Nijeriya ta yi karar shugaban Majalisar Dattawa, Godswill Akpabio, kan kin sauya matakin dakatarwar da aka yi wa Sanata Natasha Akpoti ba bisa ka’ida ba,wanda ta ce hakan take ‘yancinta ne na fadin albarkacin bakinta.

Google search engine

A kwanakin baya ne majalisar dattawa ta dakatar da Natasha Akpoti-Uduaghan na tsawon watanni shida, bayan da aka ce ta ‘yi magana ba tare da izini ba’ kuma ta ‘ki amincewa da sabuwar kujerar da aka ware mata a zauren majalisar.

A cikin karar mai lamba FHC/ABJ/CS/498/2025 da aka shigar a ranar Juma’ar da ta gabata a babbar kotun tarayya da ke Abuja, SERAP na neman da a tilasta soke dakatarwar da aka yi wa Natasha Akpoti-Uduaghan ba bisa ka’ida ba, a maido da ita, tare da dawo mata da dukkan hakkokinta.

SERAP na neman Majalisar Dattawa da ta dakatar da daukar duk wani matakin ladabtarwa a kan Natasha Akpoti-Uduaghan.

LEAVE A REPLY

Please enter your comment!
Please enter your name here

Sabbin Labarai

Za mu fara hukunta duk wani dan kasar waje da wa’adin bizarsa ya kare a Nijeriya kuma ya ci gaba da zama – Gwamnatin...

Gwamnatin Nijeriya ta bayyana cewa yanzu tana da cikakken tsarin gano tare da cafke baƙin ƙasashen waje da suka wuce wa’adin zaman da aka ba...

Obasanjo ya nuna jarumtaka da sadaukarwa wajen yi wa Nijeriya hidima – Shugaba Tinubu

Shugaban Nijeriya Bola Ahmed Tinubu, ya taya tsohon shugaban ƙasar Olusegun Obasanjo murnar cika shekaru 89 da haihuwa. A cikin wata sanarwa da mai magana da...

Mafi Shahara