DCL Hausa Radio
Kaitsaye

Iran ta samu tikitin shiga gasar cin kofin Duniya ta 2026

-

Tutar Kasar Iran 

Bayan tashi wasa chanjaras biyu da biyu tsakaninta da Uzbekistan a filin wasa na Azadi da ke Tehran a Talatar nan, Iran ta samu tikitin shiga gasar cin kofin Duniya ta 2026.

Dan wasan Iran da ke taka leda a Intermilan, Mehdi Taremi, ne ya zura kwallaye biyu bayan dawowa daga hutun rabin lokaci a fafatawar, lamarin da ya baiwa tawagar ta Iran damar shiga gasar karo na hudu a jere, jimulla karo na bakwai a tarihi. 

Google search engine

Tawagar Uzbekistan ce ta fara jan ragamar wasan bayan da Dan wasa Khojimat Erkinov ya zura kwallo a minti na 16, sai dai Taremi ya sauya lamarin a minti na 52, yanzu haka dai Iran ita ce ta farko da maki 20 a rukunin A na gasar cancantar shiga gasar cin kofin Duniya a yankin Asia.

LEAVE A REPLY

Please enter your comment!
Please enter your name here

Sabbin Labarai

Idan rikicin PDP ya ki ci, ya ki cinyewa za mu shiga kawance in ji Sule Lamido

Tsohon Gwamnan Jihar Jigawa, Alhaji Sule Lamido, ya bayyana cewa dole na iya sanyawa jam’iyyar ta shiga kawance da wasu jam’iyyu idan ƙoƙarin da ake...

‘Yan sandan Nijeriya sun sanar da dawo da aiwatar da dokar lasisin gilashin mota mai duhu

Rundunar ‘Yan Sandan Nijeriya ta sanar da cewa za ta sake fara aiwatar da dokar lasisin gilashin mota mai duhu (Tinted Glass Permit), duk da...

Mafi Shahara