DCL Hausa Radio
Kaitsaye

Iran ta samu tikitin shiga gasar cin kofin Duniya ta 2026

-

Tutar Kasar Iran 

Bayan tashi wasa chanjaras biyu da biyu tsakaninta da Uzbekistan a filin wasa na Azadi da ke Tehran a Talatar nan, Iran ta samu tikitin shiga gasar cin kofin Duniya ta 2026.

Dan wasan Iran da ke taka leda a Intermilan, Mehdi Taremi, ne ya zura kwallaye biyu bayan dawowa daga hutun rabin lokaci a fafatawar, lamarin da ya baiwa tawagar ta Iran damar shiga gasar karo na hudu a jere, jimulla karo na bakwai a tarihi. 

Google search engine

Tawagar Uzbekistan ce ta fara jan ragamar wasan bayan da Dan wasa Khojimat Erkinov ya zura kwallo a minti na 16, sai dai Taremi ya sauya lamarin a minti na 52, yanzu haka dai Iran ita ce ta farko da maki 20 a rukunin A na gasar cancantar shiga gasar cin kofin Duniya a yankin Asia.

LEAVE A REPLY

Please enter your comment!
Please enter your name here

Sabbin Labarai

Muna da hujja ba a makance muke goyon Tinubu ba – Kungiyar Disciples of Jagaban

Kungiyar magoya bayan shugaban Nijeriya Bola Ahmed Tinubu ta Disciples of Jagaban ta ce ba a makance ta ke nuna goyon baya ga shugaban ba,...

Rundunar sojin Nijeriya ta sulhunta kabilun da ke rikici a Taraba

By Salisu Ado Sulaiman Rundunar sojin kasan Nijeriya ta jagoranci zaman sulhu tsakanin kabilun da ke rikici a jihar Taraba. Kwamandan rundunar Operation Whirl Punch Brigadier Janar...

Mafi Shahara