DCL Hausa Radio
Kaitsaye

Ban da tabbacin tsayawa takarar shugaban kasa a 2027 – Atiku Abubakar

-

Alhaji Atiku Abubakar

Tsohon mataimakin shugaban kasa Atiku Abubakar ya ce baya da tabbacin ko zai tsaya takarar shugaban kasa a 2027 ba.

Google search engine

Atiku ya bayyana hakan ne a wata hira a wani shirin talabijin mai suna Untold Stories da Adesuwa Giwa-Osagie, Daily Trust ta samu.

A kwanakin baya ne tsohon dan takarar shugaban kasa a jam’iyyar PDP ya sanar da shirin yin ‘merger’ da wasu ‘yan adawa domin tunkarar zaben 2027.

Sai dai bayan bayyana kudurin na su anyi ta cece-kuce kan wanda zai jagoranci hadakar kuma ya zama dan takarar shugaban kasa, inda ake ganin tsohon dan takarar shugaban kasa na jam’iyyar Labour, Peter Obi da tsohon gwamnan jihar Kaduna, Nasir El-Rufai, a cikin manyan jiga-jigai a yayin hadakar.

Da aka tambayi Atiku ko zai tsaya takarar shugaban kasa a shekarar 2027, Atiku ya ce bai sani ba, domin da farko dole ne a samar da tsari mai kyau, fiye da kowane lokaci a tarihin siyasar kasar nan, sai dai bai janye yiyuwar tsayawa takarar ba.

LEAVE A REPLY

Please enter your comment!
Please enter your name here

Sabbin Labarai

Tsohon Gwamnan jihar Kwara Cornelius Adebayo ya rasu yana da shekaru 84

Tsohon Gwamnan jihar Kwara kuma Ministan Sadarwa na baya, Cornelius Adebayo, ya rasu yana da shekara 84 a Abuja da safiyar Laraba nan. Dansa na fari,...

An karrama ma’aikacin gwamnatin Jigawa a Saudiyya bisa dawo da kuɗin da ya tsinta

Wani ma’aikacin gudanarwa a Saudiyya, Muhammed Salalah, ya mika kwafin Alkur’ani Mai Tsarki ga Daraktan Rediyon Jigawa, Malam Isma’il Babura, a matsayin kyauta mai daraja...

Mafi Shahara