DCL Hausa Radio
Kaitsaye

Fitacciyar ‘yar jarida kuma mai fafitika a shafukan sadarwa Samira Sabo, ta yi fatan ganin an saki hambararren shugaban Nijar Mohamed Bazoum

-

‘Yar jarida a Nijar wacce ta yi fice a baya wajen sukar gwamnatin jamhuriyar ta 7 ta tsohon shugaban kasa Issoufou Mahamadou da magajinsa Mohamed Bazoum ta ziyarci gidan shugaba Issoufou Mahamadou domin taya shi murnar sakin abokan gwagwarmayar siyasarsa. 
Samira a cikin sakon da ta wallafa a shafinta na Facebook, ta ce watanni biyu da suka gabata ta samu ganawa da tsohon shugaban kasar inda ta bukaci da ya shiga cikin lamarin siyasar kasar domin samar da mafita akan dambarwar siyasar da ake ke ciki.
‘Yar jaridar ta ce a nata ra’ayi, mataki na gaba ya kasance na sakin hambararren shugaban kasar Mohamed Bazoum tare da tattaunawa da magoya bayansa har ma wadanda suke hijira a ketare.

Google search engine

LEAVE A REPLY

Please enter your comment!
Please enter your name here

Sabbin Labarai

Shugaban Amurka Donald Trumph ya haramtawa Farfesa Wole Soyinka zuwa kasar

Gwamnatin Amurka karkashin jagorancin shugaba Donald Trump ta soke takardar izinin shiga ƙasar ga Farfesa Wole Soyinka, sanannen marubuci a duniya. Farfesa Soyinka ya bayyana hakan...

Hukumar agajin gaggawa NEMA ta karɓi ƴan Nijeriya 153 da suka makale a Chadi

Hukumar ba da agajin gaggawa ta Nijeriya NEMA, ta bayyana cewa ta karɓi ’yan Nijeriya 153 da suka dawo daga ƙasar Chadi, ƙarƙashin shirin Ƙungiyar...

Mafi Shahara