HomeUncategorizedYawan maganganu kan yadda aka kubutar da janar Tsiga (Rtd) na iya...

Yawan maganganu kan yadda aka kubutar da janar Tsiga (Rtd) na iya rage kwarin gwiwar sojoji- DHQ

-

Janar Maharazu Tsiga

Hedikwatar tsaron Najeriya (DHQ) ta bayyana damuwarta kan yadda ake yada labarai cewa wasu manyan hafsoshin soja sun tara kudi domin ceto tsohon Birgediya Janar Mahrazu Tsiga (rtd), wanda ya shafe kwanaki 56 a hannun masu garkuwa.

A wata sanarwa da Daraktan Yada Labarai na rundunar, Birgediya Janar Tukur Gusau ya fitar, ya ce wannan ikirari na wani tsohon hafsan soja, Ismaila Abdullahi, na iya rage kimar aikin da rundunar Operation Fanjan Yamma ta gudanar domin ceto Janar Tsiga.

A cewar Gusau, sojojin Najeriya sun aiwatar da dogon bincike da kai samame da hare-haren sama, lamarin da ya tilasta masu garkuwan tserewa suka bar Janar Tsiga.  

Ya ce irin wadannan maganganu na iya kawo tangarda ga kwazon dakarun kasa, tare da bude kofar suka daga bangarori masu adawa da sojoji, duk da cewa bai musanta cewa an tara kudaden ba.

LEAVE A REPLY

Please enter your comment!
Please enter your name here

LATEST POSTS

Sarkin Daura ya nada Hamza Sule Sarautar Sadaukin Kasar Hausa

Maimartaba Sarkin Daura Alh Faruk Umar Faruk ya nada Hon. Hamza Sulaiman Faskari Kwamishinan mahallin jihar katsina sarautar Sadaukin Kasar Hausa a fadarsa dake garin...

Kawance domin kayar da Tinubu a 2027 ba zai yi wani tasiri ba, bata lokaci ne kawai, in ji dan jam’iyyar PDP Ayo Fayose

Tsohon gwamnan jihar Ekiti, Ayo Fayose, ya yi watsi da gamayyar jam’iyyun adawa na siyasa da ake tattaunawa a kai, da nufin kifar da Gwamnatin...

Babu wanda ya hana Kasshim Shettima shiga fadar Shugaban kasa ta Villa, labarin ba ya da tushe bare makama – Mai magana da yawunsa...

Babban Mataimaki na Musamman ga Shugaban Kasa kan Harkokin Yada Labarai Stanley Nkwocha,ya bayyana labarin da ke yawo a kafafan sada zumunta, dangane da hana...

Jiga-jigan APC sun tattaru a Abuja, sun tabbatar wa da Shugaba Tinubu zai yi nasara da gagarumin rinjaye a zaben 2027

Jiga-jigan jam’iyyar APC mai mulki sun gudanar da wani gangami a Abuja, inda suka bayyana cewa shugaba Bola Ahmed Tinubu zai samu gagarumin rinjaye a...

Most Popular

spot_img