DCL Hausa Radio
Kaitsaye

Yawan maganganu kan yadda aka kubutar da janar Tsiga (Rtd) na iya rage kwarin gwiwar sojoji- DHQ

-

Janar Maharazu Tsiga

Hedikwatar tsaron Najeriya (DHQ) ta bayyana damuwarta kan yadda ake yada labarai cewa wasu manyan hafsoshin soja sun tara kudi domin ceto tsohon Birgediya Janar Mahrazu Tsiga (rtd), wanda ya shafe kwanaki 56 a hannun masu garkuwa.

Google search engine

A wata sanarwa da Daraktan Yada Labarai na rundunar, Birgediya Janar Tukur Gusau ya fitar, ya ce wannan ikirari na wani tsohon hafsan soja, Ismaila Abdullahi, na iya rage kimar aikin da rundunar Operation Fanjan Yamma ta gudanar domin ceto Janar Tsiga.

A cewar Gusau, sojojin Najeriya sun aiwatar da dogon bincike da kai samame da hare-haren sama, lamarin da ya tilasta masu garkuwan tserewa suka bar Janar Tsiga.  

Ya ce irin wadannan maganganu na iya kawo tangarda ga kwazon dakarun kasa, tare da bude kofar suka daga bangarori masu adawa da sojoji, duk da cewa bai musanta cewa an tara kudaden ba.

LEAVE A REPLY

Please enter your comment!
Please enter your name here

Sabbin Labarai

Buhari mutum ne mai girmama al’adu da masarautu – Sarkin Musulmi

Sarkin Musulmi, Alhaji Muhammad Sa’ad Abubakar, ya shiga sahun wadanda ke jimamin rasuwar tsohon Shugaban Najeriya, Muhammadu Buhari, wanda ya rasu a wani asibiti a...

An rufe ofishin jakadancin Amurka na Abuja da Legas don jimamin rasuwat Buhari

Ofishin jakadancin Amurka da ke Abuja da kuma na Legas za su kasance a rufe a ranar Talata, 15 ga Yuli, 2025, domin girmamawa da...

Mafi Shahara