DCL Hausa Radio
Kaitsaye

Sanata Ndume na shirin shiga hadakar Atiku – Daniel Bwala

-

Daniel Bwala, mai ba shugaban kasa Bola Tinubu shawara ta musamman kan harkokin siyasa, ya ce ya kamata jam’iyyar APC ta yi hattara da Sanatan Borno ta Kudu, Ali Ndume, yana mai zargin cewa lissafin dan majalisar da ruhinsa a siyasa sun bar jam’iyyar.

Bwala ya bayyana hakan ne a wata tattaunawa da ya yi da gidan talabijin na Channels, inda yake jan hankalin jam’iyyar APC musamman shugaban jam’iyyar, Abdullahi Ganduje, cewa Sanatan na a cikin jam’iyyar, amma ruhinsa na wani waje na daban.
Inda ya kara da cewa kamata ya yi Ndume ya fice daga jam’iyyar kai tsaye kamar yadda Nasiru El-Rufai ya yi.

LEAVE A REPLY

Please enter your comment!
Please enter your name here

Sabbin Labarai

Har yanzu bamu kammala bincike ba shiyasa bamu gurfanar da El-rufa’i a gaban kotu ba – EFCC

Hukumar EFCC, mai yaki a cin hanci da rashawa a Nijeriya ta bayyana dalilin da ya sa har yanzu ba ta kai tsohon gwamnan Kaduna,...

Wanene sabon Shugaban Rundunar ‘Yan Sandan Nijeriya, Olatunji Disu?

AIG Olatunji Disu ya kasance gogaggen jami’i wanda aka nada don jagorantar rundunar 'yan sandan kasar a matsayin IGP na 23. A cewar fadar shugaban...

Mafi Shahara